ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Sun Ba Da Shawarar Gyara Tsarin Filaye Domin Dakile Matsalar Tsaro

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
2 months ago
Tsaro

Yusufu Bala Usman Institute ta gabatar da sakamakon bincike kan yadda ake tafiyar da kasa, kalubalen muhalli da kuma matsalar tsaro a Arewacin Nijeriya.

An bayyana sakamakon binciken ne a wani taron manyan masu ruwa da tsaki da aka gudanar a ranar Laraba a Jamil Hotel da ke Azare, cikin Karamar Hukumar Katagum ta Jihar Bauchi.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Zamfara
  • Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Taron ya hada mahalarta daga sassa daban-daban na Jihar Bauchi, wadda ita ce daya daga cikin jihohin Arewa hudu da aka gudanar da wannan bincike. Sauran jihohin sun hada da Jihar Jigawa, Jihar Kaduna da Jihar Katsina.

ADVERTISEMENT

Mahalarta taron sun hada da sarakunan gargajiya, shugabannin al’ummar Fulani, manoman Hausawa da kuma shugabannin addini, inda suka yi tattaunawa mai zurfi kan sakamakon binciken tare da nazarin hanyoyin magance manyan kalubalen da yankin ke fuskanta.

A yayin gabatar da binciken, Adam Higazi, wani kwararren mai bincike kan rikice-rikicen makiyaya da manoma a Nijeriya da Afirka ta Yamma, ya bayyana cewa kwace kasa da ‘yan siyasa da kamfanonin noma ke yi na daga cikin manyan dalilan da ke haddasa rasa kasa ga manoma da makiyaya a yankunan karkara.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

“Raba kasa ga manyan ‘yan siyasa da kamfanoni na haifar da sare dazuka ba tare da tsari ba, mamaye wuraren kiwo da gandun daji, da kuma toshe hanyoyin dabbobi. Wadannan su ne manyan abubuwan da ke haifar da rikici da rashin zaman lafiya a yankin,” in ji shi.

Ya kuma lura cewa al’ummomin makiyaya, musamman Fulani, na ci gaba da rasa damar samun filayen kiwo, musamman a Jihar Bauchi, sakamakon kwace filaye, lalacewar muhalli da kuma yawaitar ayyukan dan adam.

“Hakan ya sa makiyaya da dama ke barin Jihar Bauchi zuwa wasu sassan Nijeriya da ma kasashen makwabta,” in ji Dakta Higazi.

Dakta Adam Higazi ya ba da shawarar haramta sare itatuwa ba bisa ka’ida ba, da farfado da gandun daji da wuraren kiwo kamar Rigar Itas a Karamar Hukumar Itas/Gadau da kuma Udubo Grazing Reserbe, tare da sake bude hanyoyin ruwa na dabbobi a fadin jihar.

Haka kuma, ya ba da shawarar kare hakkin mallakar kasa ga kananan manoma da makiyaya baki daya.

Mai binciken ya kuma yi kira da a gyara dokar amfani da filaye (Land Use Act) tare da kafa wata hukuma ta musamman da za ta kula da matsalolin makiyaya, noma da muhalli.

A nasa jawabin, Abdullahi Umar Eggi ya ce taron ya yi niyya ne don nazari mai zurfi kan batutuwan tafiyar da kasa, lalacewar muhalli da kuma karuwar matsalar tsaro.

Ya jaddada bukatar amfani da kwarewar masu ruwa da tsaki wajen tsara manufofi masu tasiri.

Da yake magana a madadin al’ummar Fulani, Sarkin Fulanin Katagum, Alhaji Muhammad Jauro Gari, ya bukaci gwamnati da ta dauki matakin gaggawa wajen magance kalubalen da makiyaya ke fuskanta.

Ya nuna damuwa kan ci gaba da raguwar wuraren kiwo da kuma tsanantar wahalhalu da makiyayan Fulani ke ciki.

Mahalarta taron sun yi irin wannan korafi, inda suka jaddada bukatar hadin gwiwar gwamnati wajen dakile sare dazuka, dawo da hanyoyin rayuwa da kuma karfafa zaman lafiya da tsaro a Arewacin Nijeriya.

An kammala taron da kira na bai daya kan ci gaba da tattaunawa da daukar matakan manufofi masu karfi domin magance tushen rikice-rikicen kasa da kalubalen muhalli a yankin.

Hukumar kasa Birtaniya ta (UK Foreign, Commonwealth and Debelopment Office (FCDO) ta dauki nauyin gudanar da binciken ta hannun Shirin samar da zaman lafiya ta (Strengthening Peace and Resilience in Nigeria (SPRiNG).

Tsaro
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
Tsaro
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Yadda Takarar Obi Ta Zama Kamar Wani Wasan Barkwanci

Yadda Takarar Obi Ta Zama Kamar Wani Wasan Barkwanci

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.