ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Sun Ba Da Shawarar Gyara Tsarin Filaye Domin Dakile Matsalar Tsaro

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
3 months ago
Tsaro

Yusufu Bala Usman Institute ta gabatar da sakamakon bincike kan yadda ake tafiyar da kasa, kalubalen muhalli da kuma matsalar tsaro a Arewacin Nijeriya.

An bayyana sakamakon binciken ne a wani taron manyan masu ruwa da tsaki da aka gudanar a ranar Laraba a Jamil Hotel da ke Azare, cikin Karamar Hukumar Katagum ta Jihar Bauchi.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Zamfara
  • Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Taron ya hada mahalarta daga sassa daban-daban na Jihar Bauchi, wadda ita ce daya daga cikin jihohin Arewa hudu da aka gudanar da wannan bincike. Sauran jihohin sun hada da Jihar Jigawa, Jihar Kaduna da Jihar Katsina.

ADVERTISEMENT

Mahalarta taron sun hada da sarakunan gargajiya, shugabannin al’ummar Fulani, manoman Hausawa da kuma shugabannin addini, inda suka yi tattaunawa mai zurfi kan sakamakon binciken tare da nazarin hanyoyin magance manyan kalubalen da yankin ke fuskanta.

A yayin gabatar da binciken, Adam Higazi, wani kwararren mai bincike kan rikice-rikicen makiyaya da manoma a Nijeriya da Afirka ta Yamma, ya bayyana cewa kwace kasa da ‘yan siyasa da kamfanonin noma ke yi na daga cikin manyan dalilan da ke haddasa rasa kasa ga manoma da makiyaya a yankunan karkara.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

“Raba kasa ga manyan ‘yan siyasa da kamfanoni na haifar da sare dazuka ba tare da tsari ba, mamaye wuraren kiwo da gandun daji, da kuma toshe hanyoyin dabbobi. Wadannan su ne manyan abubuwan da ke haifar da rikici da rashin zaman lafiya a yankin,” in ji shi.

Ya kuma lura cewa al’ummomin makiyaya, musamman Fulani, na ci gaba da rasa damar samun filayen kiwo, musamman a Jihar Bauchi, sakamakon kwace filaye, lalacewar muhalli da kuma yawaitar ayyukan dan adam.

“Hakan ya sa makiyaya da dama ke barin Jihar Bauchi zuwa wasu sassan Nijeriya da ma kasashen makwabta,” in ji Dakta Higazi.

Dakta Adam Higazi ya ba da shawarar haramta sare itatuwa ba bisa ka’ida ba, da farfado da gandun daji da wuraren kiwo kamar Rigar Itas a Karamar Hukumar Itas/Gadau da kuma Udubo Grazing Reserbe, tare da sake bude hanyoyin ruwa na dabbobi a fadin jihar.

Haka kuma, ya ba da shawarar kare hakkin mallakar kasa ga kananan manoma da makiyaya baki daya.

Mai binciken ya kuma yi kira da a gyara dokar amfani da filaye (Land Use Act) tare da kafa wata hukuma ta musamman da za ta kula da matsalolin makiyaya, noma da muhalli.

A nasa jawabin, Abdullahi Umar Eggi ya ce taron ya yi niyya ne don nazari mai zurfi kan batutuwan tafiyar da kasa, lalacewar muhalli da kuma karuwar matsalar tsaro.

Ya jaddada bukatar amfani da kwarewar masu ruwa da tsaki wajen tsara manufofi masu tasiri.

Da yake magana a madadin al’ummar Fulani, Sarkin Fulanin Katagum, Alhaji Muhammad Jauro Gari, ya bukaci gwamnati da ta dauki matakin gaggawa wajen magance kalubalen da makiyaya ke fuskanta.

Ya nuna damuwa kan ci gaba da raguwar wuraren kiwo da kuma tsanantar wahalhalu da makiyayan Fulani ke ciki.

Mahalarta taron sun yi irin wannan korafi, inda suka jaddada bukatar hadin gwiwar gwamnati wajen dakile sare dazuka, dawo da hanyoyin rayuwa da kuma karfafa zaman lafiya da tsaro a Arewacin Nijeriya.

An kammala taron da kira na bai daya kan ci gaba da tattaunawa da daukar matakan manufofi masu karfi domin magance tushen rikice-rikicen kasa da kalubalen muhalli a yankin.

Hukumar kasa Birtaniya ta (UK Foreign, Commonwealth and Debelopment Office (FCDO) ta dauki nauyin gudanar da binciken ta hannun Shirin samar da zaman lafiya ta (Strengthening Peace and Resilience in Nigeria (SPRiNG).

Tsaro
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri
Tsaro
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Yadda Takarar Obi Ta Zama Kamar Wani Wasan Barkwanci

Yadda Takarar Obi Ta Zama Kamar Wani Wasan Barkwanci

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.