ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Sun Ba Da Shawarar Gyara Tsarin Filaye Domin Dakile Matsalar Tsaro

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
3 months ago
Tsaro

Yusufu Bala Usman Institute ta gabatar da sakamakon bincike kan yadda ake tafiyar da kasa, kalubalen muhalli da kuma matsalar tsaro a Arewacin Nijeriya.

An bayyana sakamakon binciken ne a wani taron manyan masu ruwa da tsaki da aka gudanar a ranar Laraba a Jamil Hotel da ke Azare, cikin Karamar Hukumar Katagum ta Jihar Bauchi.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Zamfara
  • Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Taron ya hada mahalarta daga sassa daban-daban na Jihar Bauchi, wadda ita ce daya daga cikin jihohin Arewa hudu da aka gudanar da wannan bincike. Sauran jihohin sun hada da Jihar Jigawa, Jihar Kaduna da Jihar Katsina.

ADVERTISEMENT

Mahalarta taron sun hada da sarakunan gargajiya, shugabannin al’ummar Fulani, manoman Hausawa da kuma shugabannin addini, inda suka yi tattaunawa mai zurfi kan sakamakon binciken tare da nazarin hanyoyin magance manyan kalubalen da yankin ke fuskanta.

A yayin gabatar da binciken, Adam Higazi, wani kwararren mai bincike kan rikice-rikicen makiyaya da manoma a Nijeriya da Afirka ta Yamma, ya bayyana cewa kwace kasa da ‘yan siyasa da kamfanonin noma ke yi na daga cikin manyan dalilan da ke haddasa rasa kasa ga manoma da makiyaya a yankunan karkara.

LABARAI MASU NASABA

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

“Raba kasa ga manyan ‘yan siyasa da kamfanoni na haifar da sare dazuka ba tare da tsari ba, mamaye wuraren kiwo da gandun daji, da kuma toshe hanyoyin dabbobi. Wadannan su ne manyan abubuwan da ke haifar da rikici da rashin zaman lafiya a yankin,” in ji shi.

Ya kuma lura cewa al’ummomin makiyaya, musamman Fulani, na ci gaba da rasa damar samun filayen kiwo, musamman a Jihar Bauchi, sakamakon kwace filaye, lalacewar muhalli da kuma yawaitar ayyukan dan adam.

“Hakan ya sa makiyaya da dama ke barin Jihar Bauchi zuwa wasu sassan Nijeriya da ma kasashen makwabta,” in ji Dakta Higazi.

Dakta Adam Higazi ya ba da shawarar haramta sare itatuwa ba bisa ka’ida ba, da farfado da gandun daji da wuraren kiwo kamar Rigar Itas a Karamar Hukumar Itas/Gadau da kuma Udubo Grazing Reserbe, tare da sake bude hanyoyin ruwa na dabbobi a fadin jihar.

Haka kuma, ya ba da shawarar kare hakkin mallakar kasa ga kananan manoma da makiyaya baki daya.

Mai binciken ya kuma yi kira da a gyara dokar amfani da filaye (Land Use Act) tare da kafa wata hukuma ta musamman da za ta kula da matsalolin makiyaya, noma da muhalli.

A nasa jawabin, Abdullahi Umar Eggi ya ce taron ya yi niyya ne don nazari mai zurfi kan batutuwan tafiyar da kasa, lalacewar muhalli da kuma karuwar matsalar tsaro.

Ya jaddada bukatar amfani da kwarewar masu ruwa da tsaki wajen tsara manufofi masu tasiri.

Da yake magana a madadin al’ummar Fulani, Sarkin Fulanin Katagum, Alhaji Muhammad Jauro Gari, ya bukaci gwamnati da ta dauki matakin gaggawa wajen magance kalubalen da makiyaya ke fuskanta.

Ya nuna damuwa kan ci gaba da raguwar wuraren kiwo da kuma tsanantar wahalhalu da makiyayan Fulani ke ciki.

Mahalarta taron sun yi irin wannan korafi, inda suka jaddada bukatar hadin gwiwar gwamnati wajen dakile sare dazuka, dawo da hanyoyin rayuwa da kuma karfafa zaman lafiya da tsaro a Arewacin Nijeriya.

An kammala taron da kira na bai daya kan ci gaba da tattaunawa da daukar matakan manufofi masu karfi domin magance tushen rikice-rikicen kasa da kalubalen muhalli a yankin.

Hukumar kasa Birtaniya ta (UK Foreign, Commonwealth and Debelopment Office (FCDO) ta dauki nauyin gudanar da binciken ta hannun Shirin samar da zaman lafiya ta (Strengthening Peace and Resilience in Nigeria (SPRiNG).

Tsaro
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas
Tsaro
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
  • Sulaiman
    Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
  • Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara
  • Sulaiman
    Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

MASU ALAKA

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara
Labarai

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi
Labarai

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
Next Post
Yadda Takarar Obi Ta Zama Kamar Wani Wasan Barkwanci

Yadda Takarar Obi Ta Zama Kamar Wani Wasan Barkwanci

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.