ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Sun Ba Da Shawarar Gyara Tsarin Filaye Domin Dakile Matsalar Tsaro

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
6 months ago
Tsaro

Yusufu Bala Usman Institute ta gabatar da sakamakon bincike kan yadda ake tafiyar da kasa, kalubalen muhalli da kuma matsalar tsaro a Arewacin Nijeriya.

An bayyana sakamakon binciken ne a wani taron manyan masu ruwa da tsaki da aka gudanar a ranar Laraba a Jamil Hotel da ke Azare, cikin Karamar Hukumar Katagum ta Jihar Bauchi.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Zamfara
  • Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Taron ya hada mahalarta daga sassa daban-daban na Jihar Bauchi, wadda ita ce daya daga cikin jihohin Arewa hudu da aka gudanar da wannan bincike. Sauran jihohin sun hada da Jihar Jigawa, Jihar Kaduna da Jihar Katsina.

ADVERTISEMENT

Mahalarta taron sun hada da sarakunan gargajiya, shugabannin al’ummar Fulani, manoman Hausawa da kuma shugabannin addini, inda suka yi tattaunawa mai zurfi kan sakamakon binciken tare da nazarin hanyoyin magance manyan kalubalen da yankin ke fuskanta.

A yayin gabatar da binciken, Adam Higazi, wani kwararren mai bincike kan rikice-rikicen makiyaya da manoma a Nijeriya da Afirka ta Yamma, ya bayyana cewa kwace kasa da ‘yan siyasa da kamfanonin noma ke yi na daga cikin manyan dalilan da ke haddasa rasa kasa ga manoma da makiyaya a yankunan karkara.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

“Raba kasa ga manyan ‘yan siyasa da kamfanoni na haifar da sare dazuka ba tare da tsari ba, mamaye wuraren kiwo da gandun daji, da kuma toshe hanyoyin dabbobi. Wadannan su ne manyan abubuwan da ke haifar da rikici da rashin zaman lafiya a yankin,” in ji shi.

Ya kuma lura cewa al’ummomin makiyaya, musamman Fulani, na ci gaba da rasa damar samun filayen kiwo, musamman a Jihar Bauchi, sakamakon kwace filaye, lalacewar muhalli da kuma yawaitar ayyukan dan adam.

“Hakan ya sa makiyaya da dama ke barin Jihar Bauchi zuwa wasu sassan Nijeriya da ma kasashen makwabta,” in ji Dakta Higazi.

Dakta Adam Higazi ya ba da shawarar haramta sare itatuwa ba bisa ka’ida ba, da farfado da gandun daji da wuraren kiwo kamar Rigar Itas a Karamar Hukumar Itas/Gadau da kuma Udubo Grazing Reserbe, tare da sake bude hanyoyin ruwa na dabbobi a fadin jihar.

Haka kuma, ya ba da shawarar kare hakkin mallakar kasa ga kananan manoma da makiyaya baki daya.

Mai binciken ya kuma yi kira da a gyara dokar amfani da filaye (Land Use Act) tare da kafa wata hukuma ta musamman da za ta kula da matsalolin makiyaya, noma da muhalli.

A nasa jawabin, Abdullahi Umar Eggi ya ce taron ya yi niyya ne don nazari mai zurfi kan batutuwan tafiyar da kasa, lalacewar muhalli da kuma karuwar matsalar tsaro.

Ya jaddada bukatar amfani da kwarewar masu ruwa da tsaki wajen tsara manufofi masu tasiri.

Da yake magana a madadin al’ummar Fulani, Sarkin Fulanin Katagum, Alhaji Muhammad Jauro Gari, ya bukaci gwamnati da ta dauki matakin gaggawa wajen magance kalubalen da makiyaya ke fuskanta.

Ya nuna damuwa kan ci gaba da raguwar wuraren kiwo da kuma tsanantar wahalhalu da makiyayan Fulani ke ciki.

Mahalarta taron sun yi irin wannan korafi, inda suka jaddada bukatar hadin gwiwar gwamnati wajen dakile sare dazuka, dawo da hanyoyin rayuwa da kuma karfafa zaman lafiya da tsaro a Arewacin Nijeriya.

An kammala taron da kira na bai daya kan ci gaba da tattaunawa da daukar matakan manufofi masu karfi domin magance tushen rikice-rikicen kasa da kalubalen muhalli a yankin.

Hukumar kasa Birtaniya ta (UK Foreign, Commonwealth and Debelopment Office (FCDO) ta dauki nauyin gudanar da binciken ta hannun Shirin samar da zaman lafiya ta (Strengthening Peace and Resilience in Nigeria (SPRiNG).

Tsaro
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas
Tsaro
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Yadda Takarar Obi Ta Zama Kamar Wani Wasan Barkwanci

Yadda Takarar Obi Ta Zama Kamar Wani Wasan Barkwanci

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.