ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masarautar Saudiyya Ta Kere Elon Musk Da Bill Gates Arziki

Arzikin Masarautar Saudiyya Ya Zarta Na Masarautar Birtaniya Sau 16

by Sadiq
2 years ago
Saudi Crown Prince Mohammed bin Salman receives The President of the United Arab Emirates, Sheikh Mohammed Bin Zayed Al-Nahyan, in Jeddah, Saudi Arabia, July 16, 2022. Saudi Press Agency/Handout via REUTERS ATTENTION EDITORS - THIS PICTURE WAS PROVIDED BY A THIRD PARTY

Saudi Crown Prince Mohammed bin Salman receives The President of the United Arab Emirates, Sheikh Mohammed Bin Zayed Al-Nahyan, in Jeddah, Saudi Arabia, July 16, 2022. Saudi Press Agency/Handout via REUTERS ATTENTION EDITORS - THIS PICTURE WAS PROVIDED BY A THIRD PARTY

Gidan Masarautar Saudiyya ya kere mamallakin X (twitter) da shugaban kamfanin Microsoft arziki a duniya, inda darajarsu ta kai dalar Amurka tiriliyan 1.4 (£1.1trillion).

MujallarForbes ta kiyasta arzikin Elon Musk, mamallakin X zuwa dala biliyan 251.3 (£ 191bn), yayin da Bill Gates, mai kamfanin Microsoft arzikinsa ya kai dala biliyan 119.6 (£93bn).

  • Wata Mata Ta Sace Jariri Sabuwar Haihuwa A Asibiti A Nasarawa
  • Harin Boko Haram Ya Yi Ajalin Mutane 7 A Yobe

Gidan sarautar Saudiyya ya hada da zuriyar Muhammad bin Saud, wanda ya kafa Masarautar Diriya a karni na 18.

ADVERTISEMENT

Iyalan masarautar sun kunshi kusan dangi 15,000 – ko da yake dukiyar masarautar mutum 2000 ne ke juya ta.

Bangaren da ke mulki a masarautar ya fito ne daga zuriyar Abdulaziz bin Abdul Rahman, wanda ya zamantar da Saudiyya.

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

Shugaban zuri’ar masarautar a yanzu shi ne Sarki Salman bin Abdulaziz Al Saud, wanda hau karagar mulki tun a shekarar 2015.

Fitaccen dansa wanda kuma shi ne magajinsa; Mohammed bin Salman, wanda aka fi sani da MBS, Yarima mai jiran gado, wanda kuma shi Firaministan Saudiyya na yanzu wanda da yawa a kasar ke kallon sa a matsayin mai juya akalar mulkin Saudiyya.

MBS da Sarki Salman suna sa ido kan abin da ya shafi tafiyar da masarautar da abin da ya shafi tauye ‘yancin jama’a da ‘yancin siyasa.

Asalin arzikinsu ya samo asali ne daga man fetur da aka samo a kasar shekaru 70 da suka gabata, wato tun a zamanin Sarki Abdulaziz bn Saud.

Masarautar Saudiyya na boye bayanan arzikinsu da yadda suke tafiyar da harkokin kudadensu, amma yadda suke kashe kudade da tafiyar da rayuwarsu ya sanya a lokuta da dama hankalin jama’a ke zuwa kan su.

A halin yanzu, harkokin kudin gidan sarautar Birtaniya na ka terere daga kafofin watsa labarai da jama’a.

Kamfanin Brand Finance ya yi wa dukiyar masarautar da Sarki Charles III ke jagoranta kimar daraja dala biliyan 88 (£69bn).

Hakan na nufin arzikin masarautar Saudiyya ya ninka na dangin Sarki Charles na III sau 16.

MASU ALAKA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Next Post
PDP A Kano: Kotu Ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Shari’ar Sadiq Wali Da Abacha

Kotu Ta Raba Auren Shekaru 7 Saboda Rashin Soyayya

LABARAI MASU NASABA

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.