• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masarautar Saudiyya Ta Kere Elon Musk Da Bill Gates Arziki

Arzikin Masarautar Saudiyya Ya Zarta Na Masarautar Birtaniya Sau 16

by Sadiq
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Masarautar Saudiyya Ta Kere Elon Musk Da Bill Gates Arziki

Saudi Crown Prince Mohammed bin Salman receives The President of the United Arab Emirates, Sheikh Mohammed Bin Zayed Al-Nahyan, in Jeddah, Saudi Arabia, July 16, 2022. Saudi Press Agency/Handout via REUTERS ATTENTION EDITORS - THIS PICTURE WAS PROVIDED BY A THIRD PARTY

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gidan Masarautar Saudiyya ya kere mamallakin X (twitter) da shugaban kamfanin Microsoft arziki a duniya, inda darajarsu ta kai dalar Amurka tiriliyan 1.4 (£1.1trillion).

MujallarForbes ta kiyasta arzikin Elon Musk, mamallakin X zuwa dala biliyan 251.3 (£ 191bn), yayin da Bill Gates, mai kamfanin Microsoft arzikinsa ya kai dala biliyan 119.6 (£93bn).

  • Wata Mata Ta Sace Jariri Sabuwar Haihuwa A Asibiti A Nasarawa
  • Harin Boko Haram Ya Yi Ajalin Mutane 7 A Yobe

Gidan sarautar Saudiyya ya hada da zuriyar Muhammad bin Saud, wanda ya kafa Masarautar Diriya a karni na 18.

Iyalan masarautar sun kunshi kusan dangi 15,000 – ko da yake dukiyar masarautar mutum 2000 ne ke juya ta.

Bangaren da ke mulki a masarautar ya fito ne daga zuriyar Abdulaziz bin Abdul Rahman, wanda ya zamantar da Saudiyya.

Labarai Masu Nasaba

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Shugaban zuri’ar masarautar a yanzu shi ne Sarki Salman bin Abdulaziz Al Saud, wanda hau karagar mulki tun a shekarar 2015.

Fitaccen dansa wanda kuma shi ne magajinsa; Mohammed bin Salman, wanda aka fi sani da MBS, Yarima mai jiran gado, wanda kuma shi Firaministan Saudiyya na yanzu wanda da yawa a kasar ke kallon sa a matsayin mai juya akalar mulkin Saudiyya.

MBS da Sarki Salman suna sa ido kan abin da ya shafi tafiyar da masarautar da abin da ya shafi tauye ‘yancin jama’a da ‘yancin siyasa.

Asalin arzikinsu ya samo asali ne daga man fetur da aka samo a kasar shekaru 70 da suka gabata, wato tun a zamanin Sarki Abdulaziz bn Saud.

Masarautar Saudiyya na boye bayanan arzikinsu da yadda suke tafiyar da harkokin kudadensu, amma yadda suke kashe kudade da tafiyar da rayuwarsu ya sanya a lokuta da dama hankalin jama’a ke zuwa kan su.

A halin yanzu, harkokin kudin gidan sarautar Birtaniya na ka terere daga kafofin watsa labarai da jama’a.

Kamfanin Brand Finance ya yi wa dukiyar masarautar da Sarki Charles III ke jagoranta kimar daraja dala biliyan 88 (£69bn).

Hakan na nufin arzikin masarautar Saudiyya ya ninka na dangin Sarki Charles na III sau 16.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bill GatesElon MuskMasarautaMasarautar birtaniyaMicrosoftSaudiyyaXYarima Salman
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wata Mata Ta Sace Jariri Sabuwar Haihuwa A Asibiti A Nasarawa

Next Post

Kotu Ta Raba Auren Shekaru 7 Saboda Rashin Soyayya

Related

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

4 hours ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

6 hours ago
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

16 hours ago
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

1 day ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

2 days ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

2 days ago
Next Post
PDP A Kano: Kotu Ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Shari’ar Sadiq Wali Da Abacha

Kotu Ta Raba Auren Shekaru 7 Saboda Rashin Soyayya

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta MiÆ™a SaÆ™on Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan ÆŠantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta MiÆ™a SaÆ™on Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan ÆŠantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.