ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Safarar Makamai Sun Faɗa Komar Ƴansanda A Kaduna

by Rabi'u Ali Indabawa
5 months ago
Kaduna

Aƙalla mutum biyar da ake zargin masu safarar makamai ne aka kama su, tare da ƙwato kusan bindigogi 30 a yayin wasu hare-haren tsaro da aka gudanar a sassa daban-daban na Jihar Kaduna.

Rundunar Ƴansandan Jihar Kaduna ta ce hare-haren sun kuma yi sanadiyyar kashe wasu da ake zargin Ƴan bindiga ne yayin artabu da jami’an tsaro.

Kwamishinan Ƴansanda, Rabiu Muhammad, ne ya bayyana hakan ranar Litinin yayin wani taron manema labarai a Kaduna, inda ya zayyano manyan nasarorin da rundunar ta samu cikin makonni biyu da suka gabata.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Kaduna Ta Raba Tiransfoma 600 Da Fitilun Sola 10,000 A Kananan Hukumomin Jihar
  • Ƙungiyar JUSUN Ta Janye Yajin Aiki Bayan Sulhu Da Gwamnatin Kaduna

Muhammad ya ce hare-haren na daga cikin matakan da ake ci gaba da ɗauka bisa sahihan bayanan sirri domin kai farmaki kan sansanonin Ƴan bindiga da maɓoyarsu a ƙananan hukumomin Kajuru, Tafa, Igabi da Kauru.

A cewarsa, an tarwatsa sansanoni da dama bayan musayar wuta mai tsanani tsakanin jami’an tsaro da Ƴan ta’adda, lamarin da ya kai ga hallaka wasu daga cikinsu, yayin da wasu suka tsere da raunukan harbi.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

“Sakamakon waɗannan hare-hare, an kama wasu fitattun Ƴan bindiga da ake nema ruwa a jallo, sannan an cafke masu safarar makamai guda biyar. Haka kuma, an ƙwato tarin makamai da alburusai,” in ji Kwamishinan.

Ya ce kayayyakin da aka ƙwato sun haɗa da bindigogi kirar AK-47 guda uku na waje, bindigogi 21 da aka ƙera a gida, bindiga kirar SMG guda ɗaya, bindigogin hannu guda biyu na waje da kuma guda huɗu da aka ƙera a gida.

Ya ƙara da cewa an kuma ƙwace tarin miyagun ƙwayoyi da ake zargin an samar wa miyagun laifuka a yayin samamen.

A wani ci gaba mai alaƙa da haka, rundunar Ƴansanda ta ce jami’an sashen yaƙi da garkuwa da mutane sun kama wani Adamu Aminu na garin Jaji a Ƙaramar Hukumar Igabi ranar 20 ga Fabrairu da misalin ƙarfe 9 na dare.

Kwamishinan Ƴansanda, Rabiu Muhammad, ya ce an samu wanda ake zargin da bindigogi ƙirar AK-47 guda shida da aka ƙera a gida, bindigogin reɓolɓer guda uku da aka ƙera a gida, bindigogin hannu guda biyu da aka ƙera a gida da kuma alburusai (magazines) na AK-47 guda bakwai na waje.

“An kuma ƙwato baƙin takalmin soja ƙirar Wellco guda ɗaya daga hannunsa. Binciken farko ya nuna cewa yana da hannu a sana’ar ƙera da safarar makamai ba bisa ƙa’ida ba, wanda ke ƙara rura wutar ayyukan laifi a ciki da wajen Kaduna State,” in ji shi.

Kwamishinan ya ƙara da cewa an kama wani da ake zargi, Abubakar Hassan na Unguwar Rogo a Ƙaramar Hukumar Jos North ta Jihar Filato, dangane da lamarin.

Muhammad ya ce bincike na ci gaba domin tarwatsa wannan ƙungiya, gano hanyoyin rarraba makaman da aka ƙwato da kuma tabbatar da cewa an hukunta duk masu hannu a ciki.

Hakazalika, Ƴansanda sun kama wasu mutum uku a Kasuwan Magani ranar 17 ga Fabrairu bisa zargin mu’amalar makamai ba bisa ƙa’ida ba.

Waɗanda ake zargin, Peter Pama da Saleh Monday duk na Iburu, da kuma Sunday Makama na Kasuwan Magani, an ce an same su da bindiga kirar AK-47 da aka ƙera a gida da kuma bindiga kirar pump-action.

“Waɗannan nasarori suna nuna jajircewarmu wajen aiwatar da aikin Ƴansanda bisa sahihan bayanan sirri da kuma ƙudurinmu na katse hanyoyin samar da makamai ba bisa ƙa’ida ba da ke rura wutar laifuka a jihar,” in ji Muhammad.

Ya sake jaddada cewa Rundunar Ƴansandan Kaduna State ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen tarwatsa ƙungiyoyin masu aikata laifi, tare da yaba wa Sufeto Janar na Ƴansanda, Kayode Egbetokun, kan jagoranci da dabarun da yake bayarwa.

Kaduna
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Martanin Da Sin Ta Mayar Kan Yunkurin Japan Ya Dace Da Muradun Duniya

Martanin Da Sin Ta Mayar Kan Yunkurin Japan Ya Dace Da Muradun Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.