ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Safarar Makamai Sun Faɗa Komar Ƴansanda A Kaduna

by Rabi'u Ali Indabawa
4 months ago
Kaduna

Aƙalla mutum biyar da ake zargin masu safarar makamai ne aka kama su, tare da ƙwato kusan bindigogi 30 a yayin wasu hare-haren tsaro da aka gudanar a sassa daban-daban na Jihar Kaduna.

Rundunar Ƴansandan Jihar Kaduna ta ce hare-haren sun kuma yi sanadiyyar kashe wasu da ake zargin Ƴan bindiga ne yayin artabu da jami’an tsaro.

Kwamishinan Ƴansanda, Rabiu Muhammad, ne ya bayyana hakan ranar Litinin yayin wani taron manema labarai a Kaduna, inda ya zayyano manyan nasarorin da rundunar ta samu cikin makonni biyu da suka gabata.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Kaduna Ta Raba Tiransfoma 600 Da Fitilun Sola 10,000 A Kananan Hukumomin Jihar
  • Ƙungiyar JUSUN Ta Janye Yajin Aiki Bayan Sulhu Da Gwamnatin Kaduna

Muhammad ya ce hare-haren na daga cikin matakan da ake ci gaba da ɗauka bisa sahihan bayanan sirri domin kai farmaki kan sansanonin Ƴan bindiga da maɓoyarsu a ƙananan hukumomin Kajuru, Tafa, Igabi da Kauru.

A cewarsa, an tarwatsa sansanoni da dama bayan musayar wuta mai tsanani tsakanin jami’an tsaro da Ƴan ta’adda, lamarin da ya kai ga hallaka wasu daga cikinsu, yayin da wasu suka tsere da raunukan harbi.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

“Sakamakon waɗannan hare-hare, an kama wasu fitattun Ƴan bindiga da ake nema ruwa a jallo, sannan an cafke masu safarar makamai guda biyar. Haka kuma, an ƙwato tarin makamai da alburusai,” in ji Kwamishinan.

Ya ce kayayyakin da aka ƙwato sun haɗa da bindigogi kirar AK-47 guda uku na waje, bindigogi 21 da aka ƙera a gida, bindiga kirar SMG guda ɗaya, bindigogin hannu guda biyu na waje da kuma guda huɗu da aka ƙera a gida.

Ya ƙara da cewa an kuma ƙwace tarin miyagun ƙwayoyi da ake zargin an samar wa miyagun laifuka a yayin samamen.

A wani ci gaba mai alaƙa da haka, rundunar Ƴansanda ta ce jami’an sashen yaƙi da garkuwa da mutane sun kama wani Adamu Aminu na garin Jaji a Ƙaramar Hukumar Igabi ranar 20 ga Fabrairu da misalin ƙarfe 9 na dare.

Kwamishinan Ƴansanda, Rabiu Muhammad, ya ce an samu wanda ake zargin da bindigogi ƙirar AK-47 guda shida da aka ƙera a gida, bindigogin reɓolɓer guda uku da aka ƙera a gida, bindigogin hannu guda biyu da aka ƙera a gida da kuma alburusai (magazines) na AK-47 guda bakwai na waje.

“An kuma ƙwato baƙin takalmin soja ƙirar Wellco guda ɗaya daga hannunsa. Binciken farko ya nuna cewa yana da hannu a sana’ar ƙera da safarar makamai ba bisa ƙa’ida ba, wanda ke ƙara rura wutar ayyukan laifi a ciki da wajen Kaduna State,” in ji shi.

Kwamishinan ya ƙara da cewa an kama wani da ake zargi, Abubakar Hassan na Unguwar Rogo a Ƙaramar Hukumar Jos North ta Jihar Filato, dangane da lamarin.

Muhammad ya ce bincike na ci gaba domin tarwatsa wannan ƙungiya, gano hanyoyin rarraba makaman da aka ƙwato da kuma tabbatar da cewa an hukunta duk masu hannu a ciki.

Hakazalika, Ƴansanda sun kama wasu mutum uku a Kasuwan Magani ranar 17 ga Fabrairu bisa zargin mu’amalar makamai ba bisa ƙa’ida ba.

Waɗanda ake zargin, Peter Pama da Saleh Monday duk na Iburu, da kuma Sunday Makama na Kasuwan Magani, an ce an same su da bindiga kirar AK-47 da aka ƙera a gida da kuma bindiga kirar pump-action.

“Waɗannan nasarori suna nuna jajircewarmu wajen aiwatar da aikin Ƴansanda bisa sahihan bayanan sirri da kuma ƙudurinmu na katse hanyoyin samar da makamai ba bisa ƙa’ida ba da ke rura wutar laifuka a jihar,” in ji Muhammad.

Ya sake jaddada cewa Rundunar Ƴansandan Kaduna State ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen tarwatsa ƙungiyoyin masu aikata laifi, tare da yaba wa Sufeto Janar na Ƴansanda, Kayode Egbetokun, kan jagoranci da dabarun da yake bayarwa.

Kaduna
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Next Post
Martanin Da Sin Ta Mayar Kan Yunkurin Japan Ya Dace Da Muradun Duniya

Martanin Da Sin Ta Mayar Kan Yunkurin Japan Ya Dace Da Muradun Duniya

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.