ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Safarar Makamai Sun Faɗa Komar Ƴansanda A Kaduna

by Rabi'u Ali Indabawa
3 months ago
Kaduna

Aƙalla mutum biyar da ake zargin masu safarar makamai ne aka kama su, tare da ƙwato kusan bindigogi 30 a yayin wasu hare-haren tsaro da aka gudanar a sassa daban-daban na Jihar Kaduna.

Rundunar Ƴansandan Jihar Kaduna ta ce hare-haren sun kuma yi sanadiyyar kashe wasu da ake zargin Ƴan bindiga ne yayin artabu da jami’an tsaro.

Kwamishinan Ƴansanda, Rabiu Muhammad, ne ya bayyana hakan ranar Litinin yayin wani taron manema labarai a Kaduna, inda ya zayyano manyan nasarorin da rundunar ta samu cikin makonni biyu da suka gabata.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Kaduna Ta Raba Tiransfoma 600 Da Fitilun Sola 10,000 A Kananan Hukumomin Jihar
  • Ƙungiyar JUSUN Ta Janye Yajin Aiki Bayan Sulhu Da Gwamnatin Kaduna

Muhammad ya ce hare-haren na daga cikin matakan da ake ci gaba da ɗauka bisa sahihan bayanan sirri domin kai farmaki kan sansanonin Ƴan bindiga da maɓoyarsu a ƙananan hukumomin Kajuru, Tafa, Igabi da Kauru.

A cewarsa, an tarwatsa sansanoni da dama bayan musayar wuta mai tsanani tsakanin jami’an tsaro da Ƴan ta’adda, lamarin da ya kai ga hallaka wasu daga cikinsu, yayin da wasu suka tsere da raunukan harbi.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

“Sakamakon waɗannan hare-hare, an kama wasu fitattun Ƴan bindiga da ake nema ruwa a jallo, sannan an cafke masu safarar makamai guda biyar. Haka kuma, an ƙwato tarin makamai da alburusai,” in ji Kwamishinan.

Ya ce kayayyakin da aka ƙwato sun haɗa da bindigogi kirar AK-47 guda uku na waje, bindigogi 21 da aka ƙera a gida, bindiga kirar SMG guda ɗaya, bindigogin hannu guda biyu na waje da kuma guda huɗu da aka ƙera a gida.

Ya ƙara da cewa an kuma ƙwace tarin miyagun ƙwayoyi da ake zargin an samar wa miyagun laifuka a yayin samamen.

A wani ci gaba mai alaƙa da haka, rundunar Ƴansanda ta ce jami’an sashen yaƙi da garkuwa da mutane sun kama wani Adamu Aminu na garin Jaji a Ƙaramar Hukumar Igabi ranar 20 ga Fabrairu da misalin ƙarfe 9 na dare.

Kwamishinan Ƴansanda, Rabiu Muhammad, ya ce an samu wanda ake zargin da bindigogi ƙirar AK-47 guda shida da aka ƙera a gida, bindigogin reɓolɓer guda uku da aka ƙera a gida, bindigogin hannu guda biyu da aka ƙera a gida da kuma alburusai (magazines) na AK-47 guda bakwai na waje.

“An kuma ƙwato baƙin takalmin soja ƙirar Wellco guda ɗaya daga hannunsa. Binciken farko ya nuna cewa yana da hannu a sana’ar ƙera da safarar makamai ba bisa ƙa’ida ba, wanda ke ƙara rura wutar ayyukan laifi a ciki da wajen Kaduna State,” in ji shi.

Kwamishinan ya ƙara da cewa an kama wani da ake zargi, Abubakar Hassan na Unguwar Rogo a Ƙaramar Hukumar Jos North ta Jihar Filato, dangane da lamarin.

Muhammad ya ce bincike na ci gaba domin tarwatsa wannan ƙungiya, gano hanyoyin rarraba makaman da aka ƙwato da kuma tabbatar da cewa an hukunta duk masu hannu a ciki.

Hakazalika, Ƴansanda sun kama wasu mutum uku a Kasuwan Magani ranar 17 ga Fabrairu bisa zargin mu’amalar makamai ba bisa ƙa’ida ba.

Waɗanda ake zargin, Peter Pama da Saleh Monday duk na Iburu, da kuma Sunday Makama na Kasuwan Magani, an ce an same su da bindiga kirar AK-47 da aka ƙera a gida da kuma bindiga kirar pump-action.

“Waɗannan nasarori suna nuna jajircewarmu wajen aiwatar da aikin Ƴansanda bisa sahihan bayanan sirri da kuma ƙudurinmu na katse hanyoyin samar da makamai ba bisa ƙa’ida ba da ke rura wutar laifuka a jihar,” in ji Muhammad.

Ya sake jaddada cewa Rundunar Ƴansandan Kaduna State ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen tarwatsa ƙungiyoyin masu aikata laifi, tare da yaba wa Sufeto Janar na Ƴansanda, Kayode Egbetokun, kan jagoranci da dabarun da yake bayarwa.

Kaduna
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Martanin Da Sin Ta Mayar Kan Yunkurin Japan Ya Dace Da Muradun Duniya

Martanin Da Sin Ta Mayar Kan Yunkurin Japan Ya Dace Da Muradun Duniya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.