ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Safarar Makamai Sun Faɗa Komar Ƴansanda A Kaduna

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
Kaduna

Aƙalla mutum biyar da ake zargin masu safarar makamai ne aka kama su, tare da ƙwato kusan bindigogi 30 a yayin wasu hare-haren tsaro da aka gudanar a sassa daban-daban na Jihar Kaduna.

Rundunar Ƴansandan Jihar Kaduna ta ce hare-haren sun kuma yi sanadiyyar kashe wasu da ake zargin Ƴan bindiga ne yayin artabu da jami’an tsaro.

Kwamishinan Ƴansanda, Rabiu Muhammad, ne ya bayyana hakan ranar Litinin yayin wani taron manema labarai a Kaduna, inda ya zayyano manyan nasarorin da rundunar ta samu cikin makonni biyu da suka gabata.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Kaduna Ta Raba Tiransfoma 600 Da Fitilun Sola 10,000 A Kananan Hukumomin Jihar
  • Ƙungiyar JUSUN Ta Janye Yajin Aiki Bayan Sulhu Da Gwamnatin Kaduna

Muhammad ya ce hare-haren na daga cikin matakan da ake ci gaba da ɗauka bisa sahihan bayanan sirri domin kai farmaki kan sansanonin Ƴan bindiga da maɓoyarsu a ƙananan hukumomin Kajuru, Tafa, Igabi da Kauru.

A cewarsa, an tarwatsa sansanoni da dama bayan musayar wuta mai tsanani tsakanin jami’an tsaro da Ƴan ta’adda, lamarin da ya kai ga hallaka wasu daga cikinsu, yayin da wasu suka tsere da raunukan harbi.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

“Sakamakon waɗannan hare-hare, an kama wasu fitattun Ƴan bindiga da ake nema ruwa a jallo, sannan an cafke masu safarar makamai guda biyar. Haka kuma, an ƙwato tarin makamai da alburusai,” in ji Kwamishinan.

Ya ce kayayyakin da aka ƙwato sun haɗa da bindigogi kirar AK-47 guda uku na waje, bindigogi 21 da aka ƙera a gida, bindiga kirar SMG guda ɗaya, bindigogin hannu guda biyu na waje da kuma guda huɗu da aka ƙera a gida.

Ya ƙara da cewa an kuma ƙwace tarin miyagun ƙwayoyi da ake zargin an samar wa miyagun laifuka a yayin samamen.

A wani ci gaba mai alaƙa da haka, rundunar Ƴansanda ta ce jami’an sashen yaƙi da garkuwa da mutane sun kama wani Adamu Aminu na garin Jaji a Ƙaramar Hukumar Igabi ranar 20 ga Fabrairu da misalin ƙarfe 9 na dare.

Kwamishinan Ƴansanda, Rabiu Muhammad, ya ce an samu wanda ake zargin da bindigogi ƙirar AK-47 guda shida da aka ƙera a gida, bindigogin reɓolɓer guda uku da aka ƙera a gida, bindigogin hannu guda biyu da aka ƙera a gida da kuma alburusai (magazines) na AK-47 guda bakwai na waje.

“An kuma ƙwato baƙin takalmin soja ƙirar Wellco guda ɗaya daga hannunsa. Binciken farko ya nuna cewa yana da hannu a sana’ar ƙera da safarar makamai ba bisa ƙa’ida ba, wanda ke ƙara rura wutar ayyukan laifi a ciki da wajen Kaduna State,” in ji shi.

Kwamishinan ya ƙara da cewa an kama wani da ake zargi, Abubakar Hassan na Unguwar Rogo a Ƙaramar Hukumar Jos North ta Jihar Filato, dangane da lamarin.

Muhammad ya ce bincike na ci gaba domin tarwatsa wannan ƙungiya, gano hanyoyin rarraba makaman da aka ƙwato da kuma tabbatar da cewa an hukunta duk masu hannu a ciki.

Hakazalika, Ƴansanda sun kama wasu mutum uku a Kasuwan Magani ranar 17 ga Fabrairu bisa zargin mu’amalar makamai ba bisa ƙa’ida ba.

Waɗanda ake zargin, Peter Pama da Saleh Monday duk na Iburu, da kuma Sunday Makama na Kasuwan Magani, an ce an same su da bindiga kirar AK-47 da aka ƙera a gida da kuma bindiga kirar pump-action.

“Waɗannan nasarori suna nuna jajircewarmu wajen aiwatar da aikin Ƴansanda bisa sahihan bayanan sirri da kuma ƙudurinmu na katse hanyoyin samar da makamai ba bisa ƙa’ida ba da ke rura wutar laifuka a jihar,” in ji Muhammad.

Ya sake jaddada cewa Rundunar Ƴansandan Kaduna State ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen tarwatsa ƙungiyoyin masu aikata laifi, tare da yaba wa Sufeto Janar na Ƴansanda, Kayode Egbetokun, kan jagoranci da dabarun da yake bayarwa.

Kaduna
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Martanin Da Sin Ta Mayar Kan Yunkurin Japan Ya Dace Da Muradun Duniya

Martanin Da Sin Ta Mayar Kan Yunkurin Japan Ya Dace Da Muradun Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.