ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matakin Soke Harajin Kwastam Ya Shaida Niyyar Kasar Sin Ta Taimakawa Kasashen Afirka A Kokarinsu Na Zamanantar Da Kansu

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
Kwastam

“Yadda kasar Sin ta soke harajin kwastam a kan kayayyakin kasashen Afirka, kyakkyawar dama ce gare mu wajen fitar da kayayyakinmu zuwa gare ta.”

“Hakan na nufin karin damammaki ga kasashen Afirka wajen bunkasa masana’antu da ma samar da karin guraben aikin yi.”

“Hakan zai ba mu fifiko ta fannin farashin kaya, haka kuma zai samar mana da karin kuzari na habaka ayyukan kere-kere da inganta kayayyakinmu……hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka, bai tsaya ga samar da gudummawa kamar yadda aka saba ba, a maimakon haka, yana taimaka wa kamfanonin kasashen Afirka samun damar sa hannu cikin ayyukan zamanantar da kasashensu.”

ADVERTISEMENT

Martani ke nan da bangarori daban daban na kasashen Afirka da suka hada da ’yan siyasa da ’yan kasuwa da masana da sauransu suka mayar, biyowa bayan yadda kasar Sin ta sanar da fara soke harajin kwastam a kan dukkannin kayayyakin da suke shigowa kasar daga kasashen Afirka 53 da suka kulla huldar diplomasiyya da ita, daga ranar 1 ga watan Mayu mai zuwa.

Dalilin da ya sa suka nuna babban yabo ga wannan matakin da kasar Sin ta dauka, shi ne saboda hakan zai biya bukatun kasashen Afirka na raya kansu, duba da cewa, kasashen Afirka sun dade suna fuskantar matsaloli ta fannin fitar da kayayyakinsu ketare, da ma karancin samun mabambantan ginshikan tattalin arziki. In mun yi nazari a kan Nijeriya, za mu gano cewa, tattalin arzikin kasar yana matukar dogara da fitar da danyen mai zuwa ketare, don haka sauyin farashin mai a duniya ya kan haifar da matsaloli ga harkokin kudi har da rayuwar al’umma a kasar. Don neman shawo kan wannan matsala, gwamnatin kasar ta gabatar da ajandar da ake kira Renewed Hope, a kokarin bunkasa tattalin arzikin kasar daga fannoni daban daban, ta yadda za a kai ga tabbatar da dorewar ci gaban tattalin arzikin kasar. A game da matakin da kasar Sin ta dauka na soke harajin kwastam a kan kayayyakin kasashen Afirka, jaridar BusinessDay ta Nijeriya a wata makalarta ta bayyana cewa, kasar Sin ita ce abokiyar ciniki mafi girma ga Nijeriya, kuma kudin ciniki a tsakanin kasashen biyu ya dada karuwa da sauri cikin ’yan shekarun baya. Matakin da kasar Sin za ta dauka na soke harajin kwastam zai kasance babbar dama ga Nijeriya wajen kara fitar da kayayyaki zuwa kasar Sin da ma kyautata tsarinta na ciniki, kuma hakan zai tabbatar da kyakkyawar makoma ga hadin gwiwar kasashen biyu.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Har ila yau, martanin da kasashen Afirka suka mayar sun kuma shaida bukatunsu game da ciniki mai adalci, musamman a yayin da wasu suka mai da hannun agogo baya a kokarin da ake yi na tabbatar da dunkulewar tattalin arzikin duniya waje daya da yaki da kariyar ciniki. A yayin da wasu kasashe suke ta da “yakin haraji” a duniya, ga shi kasar Sin ta bude kofarta ga kasashen Afirka, wanda hakan ya shaida ma’anar abokantaka. A kwanan baya, babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres shi ma ya yaba da matakin da kasar Sin ta dauka, inda kuma ya yi kira ga kasashe masu ci gaba da masu karfin tattalin arziki da su dauki irin wannan mataki.

A shekarar 2005, kasar Sin ta soke harajin kwastam a kan wasu kayayyakin da take shigowa da su daga kasashen Afirka da suka fi fama da koma bayan tattalin arziki. Ga shi yanzu, har ta kai ga soke harajin kwastam a kan dukkanin kayayyakin da take shigowa da su daga kasashen Afirka 53 da suka kulla huldar diplomasiyya da ita. Hakan ya nuna cewa kasar Sin na kara bude kofarta ga kasashen Afirka.

A bana ake cika shekaru 70 da kasar Sin ta fara kulla huldar diplomasiyya da kasashen Afirka. Cikin shekarun 70 da suka wuce, har kullum Sin da kasashen Afirka sun kasance aminan juna. Yadda kasar Sin ta soke harajin kwastam a kan dukkanin kayayyakin da take shigowa da su daga kasashen Afirka 53 da suka kulla huldar diplomasiyya da ita, ya sake isar da sako ga duniya, wato kasar Sin abokiyar tafiya ce ga kasashen Afirka a kan hanyar zamanantar da kansu. (Lubabatu)

 

 

 

 

Kwastam
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
Kwastam
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 2

Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 7

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.