ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matakin Soke Harajin Kwastam Ya Shaida Niyyar Kasar Sin Ta Taimakawa Kasashen Afirka A Kokarinsu Na Zamanantar Da Kansu

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Kwastam

“Yadda kasar Sin ta soke harajin kwastam a kan kayayyakin kasashen Afirka, kyakkyawar dama ce gare mu wajen fitar da kayayyakinmu zuwa gare ta.”

“Hakan na nufin karin damammaki ga kasashen Afirka wajen bunkasa masana’antu da ma samar da karin guraben aikin yi.”

“Hakan zai ba mu fifiko ta fannin farashin kaya, haka kuma zai samar mana da karin kuzari na habaka ayyukan kere-kere da inganta kayayyakinmu……hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka, bai tsaya ga samar da gudummawa kamar yadda aka saba ba, a maimakon haka, yana taimaka wa kamfanonin kasashen Afirka samun damar sa hannu cikin ayyukan zamanantar da kasashensu.”

ADVERTISEMENT

Martani ke nan da bangarori daban daban na kasashen Afirka da suka hada da ’yan siyasa da ’yan kasuwa da masana da sauransu suka mayar, biyowa bayan yadda kasar Sin ta sanar da fara soke harajin kwastam a kan dukkannin kayayyakin da suke shigowa kasar daga kasashen Afirka 53 da suka kulla huldar diplomasiyya da ita, daga ranar 1 ga watan Mayu mai zuwa.

Dalilin da ya sa suka nuna babban yabo ga wannan matakin da kasar Sin ta dauka, shi ne saboda hakan zai biya bukatun kasashen Afirka na raya kansu, duba da cewa, kasashen Afirka sun dade suna fuskantar matsaloli ta fannin fitar da kayayyakinsu ketare, da ma karancin samun mabambantan ginshikan tattalin arziki. In mun yi nazari a kan Nijeriya, za mu gano cewa, tattalin arzikin kasar yana matukar dogara da fitar da danyen mai zuwa ketare, don haka sauyin farashin mai a duniya ya kan haifar da matsaloli ga harkokin kudi har da rayuwar al’umma a kasar. Don neman shawo kan wannan matsala, gwamnatin kasar ta gabatar da ajandar da ake kira Renewed Hope, a kokarin bunkasa tattalin arzikin kasar daga fannoni daban daban, ta yadda za a kai ga tabbatar da dorewar ci gaban tattalin arzikin kasar. A game da matakin da kasar Sin ta dauka na soke harajin kwastam a kan kayayyakin kasashen Afirka, jaridar BusinessDay ta Nijeriya a wata makalarta ta bayyana cewa, kasar Sin ita ce abokiyar ciniki mafi girma ga Nijeriya, kuma kudin ciniki a tsakanin kasashen biyu ya dada karuwa da sauri cikin ’yan shekarun baya. Matakin da kasar Sin za ta dauka na soke harajin kwastam zai kasance babbar dama ga Nijeriya wajen kara fitar da kayayyaki zuwa kasar Sin da ma kyautata tsarinta na ciniki, kuma hakan zai tabbatar da kyakkyawar makoma ga hadin gwiwar kasashen biyu.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Har ila yau, martanin da kasashen Afirka suka mayar sun kuma shaida bukatunsu game da ciniki mai adalci, musamman a yayin da wasu suka mai da hannun agogo baya a kokarin da ake yi na tabbatar da dunkulewar tattalin arzikin duniya waje daya da yaki da kariyar ciniki. A yayin da wasu kasashe suke ta da “yakin haraji” a duniya, ga shi kasar Sin ta bude kofarta ga kasashen Afirka, wanda hakan ya shaida ma’anar abokantaka. A kwanan baya, babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres shi ma ya yaba da matakin da kasar Sin ta dauka, inda kuma ya yi kira ga kasashe masu ci gaba da masu karfin tattalin arziki da su dauki irin wannan mataki.

A shekarar 2005, kasar Sin ta soke harajin kwastam a kan wasu kayayyakin da take shigowa da su daga kasashen Afirka da suka fi fama da koma bayan tattalin arziki. Ga shi yanzu, har ta kai ga soke harajin kwastam a kan dukkanin kayayyakin da take shigowa da su daga kasashen Afirka 53 da suka kulla huldar diplomasiyya da ita. Hakan ya nuna cewa kasar Sin na kara bude kofarta ga kasashen Afirka.

A bana ake cika shekaru 70 da kasar Sin ta fara kulla huldar diplomasiyya da kasashen Afirka. Cikin shekarun 70 da suka wuce, har kullum Sin da kasashen Afirka sun kasance aminan juna. Yadda kasar Sin ta soke harajin kwastam a kan dukkanin kayayyakin da take shigowa da su daga kasashen Afirka 53 da suka kulla huldar diplomasiyya da ita, ya sake isar da sako ga duniya, wato kasar Sin abokiyar tafiya ce ga kasashen Afirka a kan hanyar zamanantar da kansu. (Lubabatu)

 

 

 

 

Kwastam
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
Kwastam
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • Sulaiman
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 2

Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 7

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.