ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matakin Soke Harajin Kwastam Ya Shaida Niyyar Kasar Sin Ta Taimakawa Kasashen Afirka A Kokarinsu Na Zamanantar Da Kansu

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Kwastam

“Yadda kasar Sin ta soke harajin kwastam a kan kayayyakin kasashen Afirka, kyakkyawar dama ce gare mu wajen fitar da kayayyakinmu zuwa gare ta.”

“Hakan na nufin karin damammaki ga kasashen Afirka wajen bunkasa masana’antu da ma samar da karin guraben aikin yi.”

“Hakan zai ba mu fifiko ta fannin farashin kaya, haka kuma zai samar mana da karin kuzari na habaka ayyukan kere-kere da inganta kayayyakinmu……hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka, bai tsaya ga samar da gudummawa kamar yadda aka saba ba, a maimakon haka, yana taimaka wa kamfanonin kasashen Afirka samun damar sa hannu cikin ayyukan zamanantar da kasashensu.”

ADVERTISEMENT

Martani ke nan da bangarori daban daban na kasashen Afirka da suka hada da ’yan siyasa da ’yan kasuwa da masana da sauransu suka mayar, biyowa bayan yadda kasar Sin ta sanar da fara soke harajin kwastam a kan dukkannin kayayyakin da suke shigowa kasar daga kasashen Afirka 53 da suka kulla huldar diplomasiyya da ita, daga ranar 1 ga watan Mayu mai zuwa.

Dalilin da ya sa suka nuna babban yabo ga wannan matakin da kasar Sin ta dauka, shi ne saboda hakan zai biya bukatun kasashen Afirka na raya kansu, duba da cewa, kasashen Afirka sun dade suna fuskantar matsaloli ta fannin fitar da kayayyakinsu ketare, da ma karancin samun mabambantan ginshikan tattalin arziki. In mun yi nazari a kan Nijeriya, za mu gano cewa, tattalin arzikin kasar yana matukar dogara da fitar da danyen mai zuwa ketare, don haka sauyin farashin mai a duniya ya kan haifar da matsaloli ga harkokin kudi har da rayuwar al’umma a kasar. Don neman shawo kan wannan matsala, gwamnatin kasar ta gabatar da ajandar da ake kira Renewed Hope, a kokarin bunkasa tattalin arzikin kasar daga fannoni daban daban, ta yadda za a kai ga tabbatar da dorewar ci gaban tattalin arzikin kasar. A game da matakin da kasar Sin ta dauka na soke harajin kwastam a kan kayayyakin kasashen Afirka, jaridar BusinessDay ta Nijeriya a wata makalarta ta bayyana cewa, kasar Sin ita ce abokiyar ciniki mafi girma ga Nijeriya, kuma kudin ciniki a tsakanin kasashen biyu ya dada karuwa da sauri cikin ’yan shekarun baya. Matakin da kasar Sin za ta dauka na soke harajin kwastam zai kasance babbar dama ga Nijeriya wajen kara fitar da kayayyaki zuwa kasar Sin da ma kyautata tsarinta na ciniki, kuma hakan zai tabbatar da kyakkyawar makoma ga hadin gwiwar kasashen biyu.

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Har ila yau, martanin da kasashen Afirka suka mayar sun kuma shaida bukatunsu game da ciniki mai adalci, musamman a yayin da wasu suka mai da hannun agogo baya a kokarin da ake yi na tabbatar da dunkulewar tattalin arzikin duniya waje daya da yaki da kariyar ciniki. A yayin da wasu kasashe suke ta da “yakin haraji” a duniya, ga shi kasar Sin ta bude kofarta ga kasashen Afirka, wanda hakan ya shaida ma’anar abokantaka. A kwanan baya, babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres shi ma ya yaba da matakin da kasar Sin ta dauka, inda kuma ya yi kira ga kasashe masu ci gaba da masu karfin tattalin arziki da su dauki irin wannan mataki.

A shekarar 2005, kasar Sin ta soke harajin kwastam a kan wasu kayayyakin da take shigowa da su daga kasashen Afirka da suka fi fama da koma bayan tattalin arziki. Ga shi yanzu, har ta kai ga soke harajin kwastam a kan dukkanin kayayyakin da take shigowa da su daga kasashen Afirka 53 da suka kulla huldar diplomasiyya da ita. Hakan ya nuna cewa kasar Sin na kara bude kofarta ga kasashen Afirka.

A bana ake cika shekaru 70 da kasar Sin ta fara kulla huldar diplomasiyya da kasashen Afirka. Cikin shekarun 70 da suka wuce, har kullum Sin da kasashen Afirka sun kasance aminan juna. Yadda kasar Sin ta soke harajin kwastam a kan dukkanin kayayyakin da take shigowa da su daga kasashen Afirka 53 da suka kulla huldar diplomasiyya da ita, ya sake isar da sako ga duniya, wato kasar Sin abokiyar tafiya ce ga kasashen Afirka a kan hanyar zamanantar da kansu. (Lubabatu)

 

 

 

 

Kwastam
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Kwastam
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”
  • Sulaiman
    Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe
  • Sulaiman
    GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara
  • Sulaiman
    Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 2

Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 7

LABARAI MASU NASABA

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.