ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matakin Soke Harajin Kwastam Ya Shaida Niyyar Kasar Sin Ta Taimakawa Kasashen Afirka A Kokarinsu Na Zamanantar Da Kansu

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
Kwastam

“Yadda kasar Sin ta soke harajin kwastam a kan kayayyakin kasashen Afirka, kyakkyawar dama ce gare mu wajen fitar da kayayyakinmu zuwa gare ta.”

“Hakan na nufin karin damammaki ga kasashen Afirka wajen bunkasa masana’antu da ma samar da karin guraben aikin yi.”

“Hakan zai ba mu fifiko ta fannin farashin kaya, haka kuma zai samar mana da karin kuzari na habaka ayyukan kere-kere da inganta kayayyakinmu……hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka, bai tsaya ga samar da gudummawa kamar yadda aka saba ba, a maimakon haka, yana taimaka wa kamfanonin kasashen Afirka samun damar sa hannu cikin ayyukan zamanantar da kasashensu.”

ADVERTISEMENT

Martani ke nan da bangarori daban daban na kasashen Afirka da suka hada da ’yan siyasa da ’yan kasuwa da masana da sauransu suka mayar, biyowa bayan yadda kasar Sin ta sanar da fara soke harajin kwastam a kan dukkannin kayayyakin da suke shigowa kasar daga kasashen Afirka 53 da suka kulla huldar diplomasiyya da ita, daga ranar 1 ga watan Mayu mai zuwa.

Dalilin da ya sa suka nuna babban yabo ga wannan matakin da kasar Sin ta dauka, shi ne saboda hakan zai biya bukatun kasashen Afirka na raya kansu, duba da cewa, kasashen Afirka sun dade suna fuskantar matsaloli ta fannin fitar da kayayyakinsu ketare, da ma karancin samun mabambantan ginshikan tattalin arziki. In mun yi nazari a kan Nijeriya, za mu gano cewa, tattalin arzikin kasar yana matukar dogara da fitar da danyen mai zuwa ketare, don haka sauyin farashin mai a duniya ya kan haifar da matsaloli ga harkokin kudi har da rayuwar al’umma a kasar. Don neman shawo kan wannan matsala, gwamnatin kasar ta gabatar da ajandar da ake kira Renewed Hope, a kokarin bunkasa tattalin arzikin kasar daga fannoni daban daban, ta yadda za a kai ga tabbatar da dorewar ci gaban tattalin arzikin kasar. A game da matakin da kasar Sin ta dauka na soke harajin kwastam a kan kayayyakin kasashen Afirka, jaridar BusinessDay ta Nijeriya a wata makalarta ta bayyana cewa, kasar Sin ita ce abokiyar ciniki mafi girma ga Nijeriya, kuma kudin ciniki a tsakanin kasashen biyu ya dada karuwa da sauri cikin ’yan shekarun baya. Matakin da kasar Sin za ta dauka na soke harajin kwastam zai kasance babbar dama ga Nijeriya wajen kara fitar da kayayyaki zuwa kasar Sin da ma kyautata tsarinta na ciniki, kuma hakan zai tabbatar da kyakkyawar makoma ga hadin gwiwar kasashen biyu.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Har ila yau, martanin da kasashen Afirka suka mayar sun kuma shaida bukatunsu game da ciniki mai adalci, musamman a yayin da wasu suka mai da hannun agogo baya a kokarin da ake yi na tabbatar da dunkulewar tattalin arzikin duniya waje daya da yaki da kariyar ciniki. A yayin da wasu kasashe suke ta da “yakin haraji” a duniya, ga shi kasar Sin ta bude kofarta ga kasashen Afirka, wanda hakan ya shaida ma’anar abokantaka. A kwanan baya, babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres shi ma ya yaba da matakin da kasar Sin ta dauka, inda kuma ya yi kira ga kasashe masu ci gaba da masu karfin tattalin arziki da su dauki irin wannan mataki.

A shekarar 2005, kasar Sin ta soke harajin kwastam a kan wasu kayayyakin da take shigowa da su daga kasashen Afirka da suka fi fama da koma bayan tattalin arziki. Ga shi yanzu, har ta kai ga soke harajin kwastam a kan dukkanin kayayyakin da take shigowa da su daga kasashen Afirka 53 da suka kulla huldar diplomasiyya da ita. Hakan ya nuna cewa kasar Sin na kara bude kofarta ga kasashen Afirka.

A bana ake cika shekaru 70 da kasar Sin ta fara kulla huldar diplomasiyya da kasashen Afirka. Cikin shekarun 70 da suka wuce, har kullum Sin da kasashen Afirka sun kasance aminan juna. Yadda kasar Sin ta soke harajin kwastam a kan dukkanin kayayyakin da take shigowa da su daga kasashen Afirka 53 da suka kulla huldar diplomasiyya da ita, ya sake isar da sako ga duniya, wato kasar Sin abokiyar tafiya ce ga kasashen Afirka a kan hanyar zamanantar da kansu. (Lubabatu)

 

 

 

 

Kwastam
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Kwastam
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 2

Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 7

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.