Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya aike da sakon taya murna ga ɗauka al’ummar Musulmi na Nijeriya a kan murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta, Annabi Muhammadu (S.A.W). A saƙon nasa, shugaban ya nemi ‘yan ƙasa da su yi amfani da wannan lokaci mai albarka don yin addu’o’i na musamman don kawo ƙarshen matsalar tsaro da ta addabi sassan ƙasar nan.
Shugaba Tinubu ya yi kira ga Musulmai da su yi koyi da kyawawan halaye da ɗabi’u na fiyayyen halitta, waɗanda suka haɗa da zaman lafiya, da hakuri, da juriya, da kuma tausayawa juna.
Ya kuma jaddada muhimmancin gina ƙasa ta hanyar bin doka da oda da kuma girmama ɗan Adam, inda ya tunatar da cewa babu inda a addini ko a ɗabi’ance aka amince da ta’addanci, ko garkuwa da mutane, ko zubar da jinin ɗan Adam.
Tinubu ya kuma roƙi al’umma da su zama masu sassauci da yin wa juna adalci domin tabbatar da ci gaban tattalin arziƙi, sannan kuma iyaye da su kula da yara su tashi tsaye wajen tarbiyyar ‘ya’yansu kan kyawawan ɗabi’u da girmama na gaba.














