ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Haifar Da Ambaliya A Libya?

by CGTN Hausa
3 years ago
Libya

A jiya ne agajin jin kai da gwamnatin kasar Sin ta samar ya isa Libya.
Bisa alkaluman da hukumar Libya ta samar a ranar 23 ga wata, an ce, mutanen da ambaliyar ta halaka wadanda aka yi rajistarsu tuni ya kai 3845. Sai dai sakamakon yadda dubban mutanen da suka bace, yawan mutanen da ambaliyar ta halaka a hakika zai zarce adadin da yawan gaske.

Munanan illolin da ambaliyar ta haifar sun kuma sa mutane sun fara tunani game da me ya haifar da wannan mummunar masifa?Wasu sun ce bala’i ne daga indallahi, amma karin mutane na ganin cewa, Amurka da sauran kasashen yamma ne ya kamata su dauki nauyinta.

  • “Mafarkina Na Zuwa Sararin Samaniya” 
  • Sin Tana Bayar Da Babbar Gudummawa Ga Gina Al’ummar Duniya Mai Makomar Bai Daya

Birnin Derna da ke gabashin kasar Libya shi yake fi fuskantar barnar da ambaliyar ke haifarwa, inda ambaliyar ta rushe wasu madatsan ruwa biyu na wurin, lamarin da ya sa ambaliyar ta lalata unguwannin birnin da dama.An ce, madatsan ruwa da suka rushe a sanadin wannan ambaliya tuni suka fara yoyo, kuma mai gudanar da madatsan ruwan da kuma masana suka yi gargadin hadarin da ake iya fuskanta.

ADVERTISEMENT

A lokacin mulkin Muammar Gaddafi, gwamnatin Libya ta taba cimma wata yarjejeniya tare da wani kamfanin kasar Turkiyya game da gyara madatsan ruwan, amma sakamakon yadda Amurka da sauran kasashen yamma suka hambarar da Libya a shekarar 2011 da sunan wai kare fararen hula daga mulkin Gaddafi, yarjejeniyar ma ta zama banza. Daga nan kuma, Libya ta tsunduma cikin yakin basasa da baraka, lamarin da ya sa aka dakushe karfin kasar, manyan ababen more rayuwa na kasar ma sun lalace, abin da kuma ya rage karfin kasar wajen rigakafin bala’u da ma tinkararsu. Da a ce tsarin hasashen bala’u na kasar na gudana yadda ya kamata, kuma an gyara madatsan ruwan cikin lokaci, da aka kai ga magance mutuwar akasarin mutanen a ambaliyar.

Libya kasa ce da ke da mafi yawan man fetur da aka gano a nahiyar Afirka, wadda ya kamata al’ummarta suka ji dadin rayuwar wadata, amma ga yanayin da suka samu kansu a ciki. Ma iya ce, Amurka da sauran kasashen yamma ne suka jefa su a cikin wannan mawuyacin hali. Kamar yadda wasu masu bibbiyar shafukan sada zumunta suka ce, “Yadda kasashen yamma suka kaddamar da yaki a Libya da ma kakaba mata takunkumi bayan yakin, sun sa wa kasar tarnaki wajen tabbatar da ci gabanta, abin da ya sa kasar da a baya ta kasance tamkar aljanna ta tsumdumma cikin wuta.”

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

“Ambaliyar da ta afkawa Derna ba safai a kan ga irinta ba a tarihi, duk da haka, kasashen yamma ne suka haifar wa al’ummar Libya wannan mummunar masifa sakamakon yadda suka kutsa cikin kasar.” (Mai Zane:Mustapha Bulama)

 

Libya
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

MASU ALAKA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
Daga Birnin Sin

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina
Daga Birnin Sin

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Next Post
Kimiyya

Masana Kimiyya Na Kasashen Kenya Da Sin Sun Kaddamar Da Kundin Farko Game Da Nau'ikan Tsirran Da Kenya Ta Wallafa

LABARAI MASU NASABA

Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje

Jagoran Matasan AAC Kwamret Yahaya Soje Ya Nemi A Saki Sowore

June 26, 2026
Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

June 26, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

June 26, 2026
Noma

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.