Bisa gayyatar shugaban kasar Sin Xi Jinping, shugaban Amurka Donald Trump zai ziyarci Sin daga yau Laraba 13 zuwa Juma’a 15 ga watan nan na Mayu.
Shugabannin kasashen biyu za su yi musayar ra’ayi mai zurfi kan manyan batutuwan da suka shafi dangantakar Sin da Amurka, da kuma zaman lafiya da ci gaban duniya. Kafin tashi daga White House, shugaba Trump ya wallafa a shafukansa na sada zumunta cewa, yana matukar shaukin ziyarar da zai kai Sin.A matsayinta na daya daga cikin dangantaka mafi muhimmanci tsakanin kasashen biyu a duniyar yau, kyakkyawar dangantakar Sin da Amurka tana da matukar muhimmanci ga zaman lafiyar duniya.
Al’ummun duniya suna da fatan cewa, ganawar shugabannin Sin da Amurka za ta ingiza dangantakarsu, ta yadda kasashen biyu za su zama sahihan abokai, tare da baiwa duniya tabbaci mai dorewa.
Tattaunawar manyan shugabannin kasashen biyu ta kasance “madogarar dangantakar Sin da Amurka”.
Tun bayan tazarcen Trump a matsayin shugaban Amurka, shugabannin Sin da Amurka sun gudanar da muhimman mu’amaloli guda 7, wanda hakan ya sa dangantakarsu ta shiga yanayi na kwanciyar hankali. To sai dai kuma a halin yanzu, ana fuskantar sauye-sauye cikin sauri irin wadanda ba a taba gani ba a karnin da ya gabata, ana fama da yanayin duniya mai sarkakiya da rashin dorewa, don haka ganawar shugabannin kasashen biyu ita kanta, tana dauke da kyakkyawan sako ga duniya.
Duniya tana da girma irin wadda za ta iya daukar ci gaban Sin da Amurka tare da wadatar kowannensu.
Ana fatan cewa, ganawar shugabannin Sin da Amurka za ta ci gaba da jagorantar ci gaban huldarsu bisa kwanciyar hankali da dorewa, da kuma samar da yanayi na lumana da tabbaci mai muhimmanci ga duniya mai fuskantar sauye-sauye da rikice-rikice. (Amina Xu)














Discussion about this post