ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Kasashe Da Yawa Ke Warware Tasirin Dalar Amurka?

by CMG Hausa
3 years ago
Amurka

A cikin kwanakin baya, kasashe da dama na daukar matakai a kokarin warware tasirin dalar Amurka, ciki har da kasashen Latin Amurka, da na gabas ta tsakiya, sai kuma kasashen ASEAN, da Rasha da Iran, har ma da wasu kasashen Turai, bi da bi sassan suna ta bullo da shirye-shiryensu, ko kuma daukar matakai, don neman gudanar da ciniki da kudaden da ba dalar Amurka ba. A Afirka ma, gwamnatin Kenya ta sanar da yin watsi da dalar Amurkar wajen shigar da makamashi, inda har ta cimma yarjejeniya da kasar Saudiyya, kan sayen makamashi da kudinta na shilling. Ita kuwa ministar harkokin wajen kasar Afirka ta kudu Naledi Pandor cewa ta yi, kasashen kungiyar BRICS na nazarin kafa wani tsarin ciniki mai adalci bisa bankin NDB wanda aka kafa a shekarar 2014, ta yadda za a kai ga warware tasirin dalar Amurka. 

Amma me ya sa kasashen ke wannan kokari? Lallai tun bayan da dalar Amurka ta kafa babakere a duniya bisa tsarin Bretton Woods da aka kafa a shekarar 1944, kasashen duniya sun sha wahalhalun da dalar ta haifar musu. Kasancewar dala muhimmin kudin da aka fi yin amfani da shi wajen gudanar da ciniki tsakanin kasa da kasa, Amurka ta sha yin amfani da dala wajen kakaba takunkumi a kan wasu kasashen da suka ki biyayya gare ta, baya ga yadda ta rika cusa matsalolin tattalin arzikinta ga sauran kasashen duniya, tare da kwace arzikinsu ta hanyar daidaita kudin ruwa kan dala.

  • Wariyar Launin Fata Da Amfani Da Makamai Barkatai Ne Ke Rura Wutar Harbe-Harben Kan Mai Tsautsayi A Amurka

Idan ba a manta ba, bayan aukuwar rikici tsakanin Ukraine da Rasha, Amurkar ta hada kan kasashe da dama wajen kakaba wa Rashan takunkumi, matakin da ya haifar da mummunan tasiri ga cinikin fitar da hajojin kasar, kuma hakan ya nuna yadda take amfani da dalarta a matsayin makami na nuna fin karfi.

ADVERTISEMENT

Sai kuma daga watan Maris na bara, asusun ajiyar kasar Amurka ya sha daga kudin ruwa har sau tara, a yunkurin daidaita matsalar hauhawar farashin kaya da take fuskanta a gida, matakin da ya haifar da hauhawar farashin kaya, da tabarbarewar tattalin arziki a kasashen duniya da dama. Kamar dai yadda yadda tsohon sakataren kudin kasar ta Amurka John Connally ya fada, “dala kudinmu ne, amma kuma matsala ce gare ku.”

A gabanin yadda kasashen duniya ke daukar matakai na warware tasirin dala, dan majalisar dattawa daga jihar Florida Marco Rubio, ya bayyana bakin cikin sa yana cewa, “Nan da shekaru biyar masu zuwa, babu zancen takunkumi, kasancewar karin kasashe na ciniki da kudin da ba dala ba, a gaba ba wani mataki da za mu iya dauka don sanya musu takunkumi.”

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Abin haka yake, zamanin da Amurka ke amfani da dalarta wajen kafa babakere a duniya na dab da karewa, kuma ya kamata ‘yan siyasa irinsu Marco Rubio, su yi tunani sosai a kan me ya sa sassan kasa da kasa ke neman warware tasirin dala. In dai har Amurka ta ci gaba da nuna fin karfi da babakere, kuma ta gudanar da harkoki ba bisa ka’idojin duniya ba, tare da haifar da mumunnan tasirin ga tattalin arzikin duniya, to, tabbas za ta ga bayan matsayin dalarta. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

 

 

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Amurka Za Ta Iya Daidaita Batun Bazuwar Bayanan Sirri Kuwa?

Amurka Za Ta Iya Daidaita Batun Bazuwar Bayanan Sirri Kuwa?

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.