ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Taron JKS Da Ake Yi Ya Jawo Hankalin Duniya

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 years ago
JKS

A jiya ne kasar Sin ta fitar da alkaluman tattalin arzikinta na rabin farko na shekarar bana, inda yawan GDPn kasar ya zarce yuan triliyan 61, adadin da ya karu da kashi 5 cikin dari, idan aka kwatanta da makamancin lokacin a bara. Lallai, yadda kasar Sin ke kokarin neman sauye-sauye, yana ta samar da babban karfi ga tattalin arzikinta. 

A wannan rana kuma, kasar Sin ta kara tashoshin kwastam 37 da ke iya kula da bakin da suke yada zango a kasar cikin sa’o’i 144 ba tare da samun biza ba, a yayin da batun “China Travel” ke matukar samun karbuwa daga wajen baki, wanda hakan ya zama karin matakin da ke samar da sauki ga baki da ke zuwa nan kasar Sin, haka kuma karin mataki ne da kasar Sin ta dauka na kara bude kofarta ga ketare, wanda tabbas zai jawo karin baki zuwa nan kasar don more damammakinta.

  • Kasuwar Hayakin Carbon Ta Kasar Sin Tana Da Karko
  • Amurka: Sarkin Leken Asiri Na Neman Habaka Karfinta

A hakika, tun bayan da kasar Sin ta fara aiwatar da manufar yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga ketare a shekarar 1978, kasar ta samu gaggaruman nasarori wajen bunkasuwar tattalin arziki da zaman al’umma, kuma alkaluman tattalin arzikin da aka samar, da bunkasar harkokin “China Travel” da ke matukar samun karbuwa, duka sun shaida hakan. Al’amuran da suka wakana sun yi ta shaida cewa, manufar yin gyare-gyare a cikin gida da bude kofa ga kasashen ketare, muhimman matakai ne da kasar Sin ta dauka na zamanintar da kanta.

ADVERTISEMENT

A kuma jiya ne aka kaddamar da cikakken zama na uku na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin ko (JKS) karo na 20, taron da ya jawo hankalin kasa da kasa, amma me ya sa hakan?

A kan gudanar da babban taron wakilan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin a shekaru biyar-biyar, kuma a tsakanin duk tarukan wakilan biyu, kwamitin kolin JKS ya kan kira cikakken zamansa har sau bakwai. A rahoton da kamfanin dillancin labarai na Bloomberg ya bayar, ya ce daga cikin tarukan da JKS take gudanarwa a kai a kai, cikakken zama karo na uku na da matukar muhimmanci, sakamakon irin tasirin da ya kan haifar ga kasar da ta zama ta biyu a duniya wajen karfin tattalin arziki. Har ila yau kuma a cewar kafar BBC, cikakken zama da kwamitin kolin JKS ya gudanar a karo na uku yana da ma’anar musamman a tarihin jam’iyyar. Tun bayan da kasar Sin ta fara aiwatar da manufar yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga kasashen ketare, cikakken zama karo na uku da kowane kwamitin kolin JKS ya gudanar ya kan mai da hankali a kan yin gyare-gyaren tattalin arziki, wanda kuma ke taka muhimmiyar rawa ga bunkasuwar kasar Sin. Ana kuma sa ran tsara manyan manufofin da suka shafi gyare-gyaren tattalin arziki a wajen taron.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Lallai haka abun yake. Kasar Sin ta dauki manufar yin gyare-gyare a cikin gida da bude kofa ga kasashen ketare ne a gun cikakken zama karo na uku na kwamitin kolin JKS karo na 11 da aka gudanar a shekarar 1978, kuma tun daga lokacin, batun gyare-gyare ya zama babban jigo ga cikakken zama na uku da kowane kwamitin kolin JKS ya kira. Manufar yin gyare-gyare a cikin gida, da bude kofa ga kasashen ketare, ta samar da manyan sauye-sauye ga kasar Sin, haka kuma ta haifar da babban tasiri ga duniya. A gun zaman taron da ake yi a wannan karo, za a tsara ayyukan da za a yi wajen zurfafa gyare-gyare daga dukkan fannoni a kokarin da ake yi na zamanintar da kasar Sin, matakin da zai samar da alkiblar ci gaban kasar a gaba, tare da samar da karin damammaki ga kasashen duniya da ke fuskantar kalubaloli iri daban daban.

Tun bayan da kasar Sin ta fara aiwatar da manufar yin gyare-gyare a cikin gida da bude kofa ga kasashen ketare, kasar ta zamanto kasa ta biyu mafiya karfin tattalin arziki a duniya, kuma karfin kasar da ma tasirinta a duniya sun karu kwarai da gaske. A yayin da wasu kasashe suke yunkurin rufe kofarsu ga sauran kasashen duniya, zaman taron da JKS ke yi ya shaida wa duniya cewa, kasar Sin za ta nace ga bin hanyar yin gyare-gyare a cikin gida da bude kofa ga kasashen ketare, don kara amfanar da al’ummar kasashen duniya. Daidai da kalaman Hassan Ragab, shehun malami a jami’ar SCU ta kasar Masar, wanda ya ce taron da ake yi zai shaida niyyar kasar Sin ta zurfafa gyare-gyare daga dukkan fannoni, da ma zamanintar da kanta, kuma bisa tsarin hadin gwiwar shawarar “ziri daya da hanya daya”, zai sa kaimin bunkasuwar tattalin arzikin duniya.

A sa’i daya kuma, bisa ga nasarorin da kasar Sin ta cimma, yanzu haka kasashen duniya sun san cewa ba hanya daya kacal ake iya bi wajen zamanintar da kai ba, kuma taron da ake yi zai kara shaida wa duniya hanyoyin da kasar Sin za ta bi wajen zamanintar da kanta, wanda hakan ke da matukar ma’ana ga kasashe masu tasowa har ma da duniya baki daya.

Kasar Sin na kan hanyar zuwa inda ta yi niyya, kuma tana samar da kwarin gwiwa da damammaki ga duniya, kuma za ta dada samar da kuzari ga duniya bisa ga yadda take yin gyare-gyare a cikin gida da bude kofa ga kasashen duniya.

JKS
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    “Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa
  • Sulaiman
    Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya
  • Sulaiman
    Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
JKS
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Fahimtar Manufar Kasar Sin Ta Yin Kwaskwarima A Sabon Zamani: Kokarin Koya Da Kuma Mallakar Fasahohi Daga Sauran Kasashen Waje

Fahimtar Manufar Kasar Sin Ta Yin Kwaskwarima A Sabon Zamani: Kokarin Koya Da Kuma Mallakar Fasahohi Daga Sauran Kasashen Waje

LABARAI MASU NASABA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026
Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

September 9, 2026
Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

September 9, 2026
Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa

Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa

September 9, 2026
’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.