Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN), ya rawaito cewa an samu ɓullar cutar ne a Jihar Cross River kamar yadda ya Kwamishinan Lafiya na jihar, Dakta Henry Ayuk, ya bayyana a taron manema labaru da ya gudana a yau Talata 21 ga watan Afirilu a babban birnin jihar Calabar.
Kwamishinan ya ce an samu cutar ne ta dalilin wani ɗan ƙasar China, wanda ya ke aiki da kamfanin Lafarge, bayan da ya dawo daga ƙasar sa a ranar 17 ga watan Maris na wannan shekarar, sannan ya fara nuna alamunta a ranar 10 ga watan Afirilu .
“Kwamishinan ya ce bayan an gwada samfurin asibitin koyarwa na UCTH, da kuma duba duk wata ka’ida an tabbatar da yana da cutar Korona mai samfurin covid-19”
Kwamishinan ya ce gwamnatin jihar karkashin da ma’aikatarsa sun ɗauki matakin da ya kamata domin ganin an keɓe mutanen da sukayi mu’amala da shi a tsakanin lokutan da ya dawo da kuma lokacin da ya zauna a tsakanin sati 3 da ya yi a Nijeriya.















Discussion about this post