ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mummunan Zato

by Sulaiman Bala Idris and Sulaiman
7 months ago
Mummunan zato

Kowa ma ya san zato zunubi ne, ko da kuwa ya zamo gaskiya. Duk da haka, mutanen wannan duniya sun toshe kofofin zukatansu wurin hana ma zato yin zaman dirshan. Da yawa ma zukatan na su a bude su ke su na marhaba da wani al’amari wanda za su yi zato a cikinshi. Wuce nan ma, wasu farautar laifuka ko bibiyan mutane don su zargi ayyukansu su ke yi.

Mutane dabi’unsu daban daban ne, sai dai babu wata dabi’a wacce ba a iya rusa ta ko a gina ta. Shi ne ma ya fi dacewa ga iyaye su zama maluman farko wurin shigar da dabi’u ga dansu. Misali, akwai wani sarki mai suna Akbar a yankin indiya wanda ya rayu a tsakankanin shekarar 1542 zuwa 1602 wanda ya ke son samun tabbaci akan jijitar wai idan a ka haifi yaro ya zama ba a koyar da shi kowanne harshe ba, zai girma ne ya na mai magana da harshen Yahudanci. Sai sarkin ya sa a ka kebe mi shi wasu jarirai guda goma. Da jariran su ka girma sai ya zama ba su iya kowanne harshe (sabanin cewa za su tashi da yaren Yahudanci), haka nan kuma dabi’unsu irin na dabbobi. Hatta tafiya ba su iya yi sai dai rarrafe kamar yadda tumaki ke yi.

Wannan nazari kadai ya isa ya gamsar da mu cewa duk mutumin da mahaifanshi su ka wawaitar da yarintarshi ya na iya girman sakarci da dabi’u rikitattu. Ko kuma ya hadu da wasu su jibga mishi irin tasu dabi’ar. A nan za mu iya karkasa dabi’un mutane mu ware masu kyau da marasa kyau.

ADVERTISEMENT

A hannu daya sai mu ce dabi’u masu kyau natijarsu na komawa zuwa ga iyaye ne, marasa kyau ma na komawa gare su ne.

Kyautata zato da munana zato dukkaninsu dabi’u ne wadanda ke kishiyantar juna. Haka nan kuma ya na da kyau mu fahimci cewa dabi’u guda biyu wadanda ke karo da juna (kishiyoyi) ba su taba haduwa a lokaci guda wurin tasirantuwa ga mutum.

LABARAI MASU NASABA

Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

Nakasa A Mahangar Karin Magana: Guzurin Ranar Nakasassu Ta Duniya

Ko dai ka kasance mai mummunar dabi’a ko kuma mai kyakkyawa. Kamar dabi’ar fushi ne, ai ba zai yiwu a samu wani mutum mai masifaffen fushi ba, sannan kuma a lokaci guda mai tsananin hakuri.

Idan ka ga mutum ya na kyautatawa mutane zato a mu’amalolinshi da su, babu mamaki ko kadan akan cewa iyayenshi mutane ne masu kyautata zato. Mafi yawan lokuta idan kuma ka ga wani na munana zato a kodayaushe, to iyayenshi ma ta na iya yiwuwa halinsu kenan.

Tun ice na danye a ke lankwasa shi. Dalilan da su ka sa a tashin farko na fara da zargin iyaye shi ne; su ne mutanen farko da linzamin rayuwar dansu ke a hannunsu. Idan sun kasance masu hikima da hangen nesa, dansu zai kwaikwayo hikima da hangen nesar nan ta su.

Daga cikin matakan da ya kamata iyaye su dauka don kauracewa dansu dabi’ar munana zato sun kunshi daina zargi. Kar iyayen su rika yawan zargi, ta yadda har dansu zai iya koyo. Zargi a nan na nufin kar mata ta rika zargin mijinta ba gaira ba dalili, shi ma mijin haka.

Sannan kuma idan har wani abu ya faru wanda iyayen ba su da tabbaci ko hakikani sai su ci gaba da bincike don samun sahihanci ko kuma su fita batun maganar kawai kwata kwata. Idan ba haka ba dan su zai girma da yawo da jita jita da saurin lakaba ma mutane zantukan da ba gaskiya ba.

Duk wannan misalin ina kokarin nuna rawar da iyaye za su iya takawa ne wurin shigar da dabi’ar kyautata zato ga ‘ya ‘yansu, cikin ruwan sanyi ba tare da wani wahala ba.

A wannan zamanin da mu ke ciki munana zato na daya daga ‘yan sahun gaban al’amuran da ke tsinke igiyar aure. Munana zaton na farawa ne daga zargi; idan zargin ya yi yawa sai zuciya ta fara shigo da zato, a haka zaton zai ta girma har ya zama mummuna, sai a nemi aure a rasa.

Munana zato har walayau shi ne ke gina katangar karfe tsakanin ubangida da yaronshi. A wasu lokutan matsala ce kankanuwa wacce ba ta bukatar sa’o’i (hours) an magance ta, amma sakamakon munana zato sai ta kai ga an yi rabuwar tsiya.

Babban matsalar mutumin da ke munana zato shi ne halinshi ba halin kwarai ba ne. bincike ma ya nuna cewa da yawa wadanda ke saurin munana zato ba tare da bincike ba, su na yin haka ne saboda abun da su ke zato a kai aikinsu ne.

Wani abu da masu wannan mugun hali ba su fahimta ba shi ne, idan mutum ya yi nisa a harkar munana zato abun na rika a zuciyarshi ne. ta yadda ko akan idonshi a ka assasa wani aikin alheri, zai ce sharri ne.

Idan ka na so ka taimaki kanka ka daina munana ma mutane zato, shi ya fi komi sauki ga duk mai son dainawa, amma kuma akwai wahala ga wanda ya rika a harkar. Kawai sai ka daina bibiyan ayyukan mutane, musamman ma abubuwan da babu ruwanka a cikinsu. Sannan ka sa alheri a zuciyarka sama da sharri, idan ka yi haka, za ka tsira daga mummunan zato.

Mummunan zato
Sulaiman Bala Idris
+ posts Bio
  • Sulaiman Bala Idris
    https://hausa.leadership.ng/author/sulaiman-bala-idris/
    ‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa
  • Sulaiman Bala Idris
    https://hausa.leadership.ng/author/sulaiman-bala-idris/
    Hayaniya ‘Yar Facebook!
  • Sulaiman Bala Idris
    https://hausa.leadership.ng/author/sulaiman-bala-idris/
    Me Ake Nufi Da Ado? 
  • Sulaiman Bala Idris
    https://hausa.leadership.ng/author/sulaiman-bala-idris/
    Gwamna Dauda Lawal A Shekara 60: Inda Akwai Fata, Akwai Mafita
Mummunan zato
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba
Muƙala

Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

June 30, 2025
Nakasa A Mahangar Karin Magana: Guzurin Ranar Nakasassu Ta Duniya
Muƙala

Nakasa A Mahangar Karin Magana: Guzurin Ranar Nakasassu Ta Duniya

December 3, 2024
Khalifan Sheikh Ibrahim Inyas Daga Ƙasar Sanigal Ya Goyi Bayan Sunusi Lamido Sunusi II
Al'adu

Khalifan Sheikh Ibrahim Inyas Daga Ƙasar Sanigal Ya Goyi Bayan Sunusi Lamido Sunusi II

May 27, 2024
Next Post
Kofin Duniya

Kasashe Nawa Ne Suka Samu Tikitin Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026
Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.