ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashe Nawa Ne Suka Samu Tikitin Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
10 months ago
Kofin Duniya

Kawo yanzu dai mafarkin Nijeriya ya kare game da batun zuwa gasar kofin duniya ta 2026 bayan ta sha kashi a hannun Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo a ranar Lahadi. Hakan na nufin cewa Nijeriya ba za ta halarci gasar ba karo na biyu a jere.

Kasashen Scotland da Belgium da Croatia sun kasance kasashen da a baya-bayan nan daga nahiyar Turai da suka samu gurbi a Gasar ta Kofin Duniya ta 2026 da za a yi a kasashen Amurka da Medico da kuma Canada.

Kawo yanzu kasashe 42 sun samu gurbi, da suka hada da Ingila da Faransa da Portugal da Norway da Jamus da Crotia da Netherlands Argentina mai rike da kofin da Cape Berde bakin gasar da Jordan da kuma Uzbekistan.

ADVERTISEMENT

 

Masu Masaukin Baki: Canada, Mexico, United States.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

 

Yankin Asia: Australia, Iran, Japan, Jordan, Katar, Saudi Arabia, South Korea, Uzbekistan Nahiyar Afirka: Algeria, Cape Berde, Egypt, Ghana, Ibory Coast, Morocco, Senegal, South Africa, Tunisia.

 

Concacaf: Curaçao, Haiti, Panama.

 

Nahiyar Turai: Austria, Belgium, Croatia, England, France, Germany, Netherlands, Norway, Portugal, Scotland, Spain, Switzerland.

 

Yankin Oceania: New Zealand

 

Kudancin Amurka: Argentina, Brazil, Colombia, Ecuador, Paraguay, Uruguay.

 

Ya zuwa yanzu akwai gurabe 18 da suka rage a gasar, da yawa daga cikinsu kuma daga nahiyar Turai ne.

Australia da Iran da Japan da Jordan da Katar da Saudiyya da Koriya ta Kudu duka sun samu gurabe daga yankin Asiya. New Zealand ta samu gurbi guda daya da aka ware wa yankin Oceania.

 

Daga nahiyar Afirka kuwa, Tunisiya da Morocco ne suka fara samun gurbi a gasar, daga baya kuma kasashen Aljeriya da Cape Berde da Masar da Ghana da Ibory Coast da Senegal da kuma Afirka ta Kudu – wadda za ta buga gasar karon farko tun 2010 da ta karbi bakuncin gasar.

 

A yankin Kudancin Amurka kuwa kasashen Brazil da Ecuador da Uruguay da Paraguay kuma Colombia na daga cikin kasashen yankin da suka samu gurbi ya zuwa yanzu.

Duk da cewa kasashen, Bolibia da New Caledonia ba su samu gurbi kai-tsaye ba, amma za su buga wasannin neman gurbi na nahiyoyi a watan Maris na 2026.

 

Kasashen da suka samu gurbin Gasar Kofin Duniya ta 2026

Masu Masaukin Baki: Canada, Medico, United States

Yankin Asia: Australia, Iran, Japan, Jordan, Katar, Saudi Arabia, South Korea, Uzbekistan

Nahiyar Afirka: Algeria, Cape Berde, Egypt, Ghana, Ibory Coast, Morocco, Senegal, South Africa, Tunisia

Concacaf: Curaçao, Haiti, Panama

Nahiyar Turai: Austria, Belgium, Croatia, England, France, Germany, Netherlands, Norway, Portugal, Scotland, Spain, Switzerland.

 

Yankin Oceania: New Zealand

Kudancin Amurka: Argentina, Brazil, Colombia, Ecuador, Paraguay, Uruguay

Ya tsarin wasannin neman gurbin yake?

Kowace daya daga cikin hukumar kwallon kafa ta FIFA ta nahiyoyi na amfani da hanya ta daban domin tantance kasar da za ta samu gurbin Gasar Kofin Duniyar da ake yi duk bayan shekara hudu.

Oceania ne yanki daya da ya kammala nasa wasan neman gurbin, wanda dama gurbi daya aka tanadar masa.

Daga cikin tawagogi 48 da za su halarci gasar, tuni aka ware wa kasashe ukun da za su karbi bakuncin gasar gurabe, sai kuma gurabe 43 da sauran kasashen duniya za su samu ta hanyar samun gurbi kai-tsaye, daga nahiyoyin duniya shida.

Sai kuma ragowar gurabe biyu da za a samu ta hanyar buga wasannin cike gurbi tsakanin nahiyoyin.

 

Nahiyar Turai

Guraben da aka ware wa nahiyar: 16

Kasashen da suka samu gurbi kawo yanzu: Croatia, England da France da Portugal da Netherland da Sifaniya da Belgium da Jamus da Norway.

An raba kasashen nahiyar zuwa rukuni 12, wadanda suka kare a mataki na daya a kowane rukuni za su samu gurbi kai-tsaye don zuwa gasar. Su kuma kasashe 12 da suka kare a mataki na biyu a rukunonin, za su buga wasannin cike gurbi, tare da kasashe hudu da suka fi yawan maki a matakin rukuni na gasar UEFA Nations League da ba su samu gurbin zuwa Kofin Duniyar ba.

A cikinsu ne za a tantance kasashe hudu da za su samu karin guraben nahiyar Turai a Gasar Kofin Duniyar. Turai ce kawai nahiyar ba ta da wakilci a gasar cike gurbi ta nahiyoyi.

 

Kudancin Amurka

Guraben da aka ware wa nahiyar: Shida, da kasa daya da za ta buga gasar cike gurbi ta nahiyoyi

Kasashen da suka samu gurbi: Argentina, Brazil, Colombia, Ecuador, Paraguay da kuma Uruguay.

Wadda za ta je gasar cike gurbi ta nahiyoyi: Bolibia, Yankin Asia.

Guraben da aka ware wa nahiyar: Takwas, da kasa daya da za ta buga gasar cike gurbi ta nahiyoyi.

Kasashen da suka samu gurbi: Australia, Iran, Japan, Jordan, Katar, Saudi Arabia, South Korea da Uzbekistan Kasashen UAE da Iraki za su kara tsakaninsu don tantance wadda za ta je gasar cike gurbi ta nahiyoyi.

 

Nahiyar Afirka

Guraben da aka ware wa nahiyar: Tara, da kasa daya da za ta buga gasar cike gurbi ta nahiyoyi.

Kasashen da suka samu gurbi: Algeria, Cape Berde, Egypt, Ghana, Ibory Coast, Morocco, Senegal, Afirka ta Kudu da Tunisiya. Kasar da za ta je gasar cike gurbi ta nahiyoyi: DR Congo

Arewaci da tsakiyar Amurka da yankin Caribbean

Guraben da aka ware wa yankunan: Shida (ciki har da ukun da za su karbi bakunci), da kasashe biyu da za su buga gasar cike gurbi ta nahiyoyi.

Kasashen da suka samu gurbi: Canada, Medico da Amurka, wadanda suka samu kai-tsaye.

 

Yankin Oceania

Guraben da aka ware wa yankin: Daya, da kasa daya da za ta buga gasar cike gurbi ta nahiyoyi.

 

Kasar da ta samu gurbi: New Zealand

Kasar New Caledonia, za ta buga gasar cike gurbi ta nahiyoyi – wadda ta kunshi kasashe daga Afirka da Asia da kudancin Amurka da Arewacin Amurka.

Kofin duniya
Abba Ibrahim Wada
Website |  + posts Bio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso
Kofin duniya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Munafunci Dodo Ya Kan Ci Mai Shi

Munafunci Dodo Ya Kan Ci Mai Shi

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.