Wata babbar kotu a Kano, ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ga wani mai suna Abdulaziz Umar, da ya daba wa wani mai suna Mubarak Salisu, wuka har lahira.
A jiya ne, aka yanke wa Umar wanda ke zaune a unguwar Fagge a Kano, hukunci bisa laifuka biyu da suka hada da fashi da makami da kuma kisan kai.
Da take yanke hukuncin, mai shari’a Zuwaira Yusuf, ta ce; masu gabatar da kara sun tabbatar da laifin nasa, ba tare da wata shakka ba.
“Na yanke hukuncin daurin rai-da-rai ga wanda aka samu da laifin yin fashi da kuma kisa ta hanyar rataya, saboda kisan kai, har sai an tabbatar da mutuwarsa,” in ji ta.
Tun da farko, lauya mai shigar da kara, Aisha Salisu, ta shaida wa kotun cewa; wanda ake tuhuma ya aikata laifin ne a ranar 1 ga Oktoban 2020, a Race Course, Badawa Layout a Kano.
Ta ce, a wannan ranar ne, Umar ya yi sanadiyyar mutuwar Salisu, ta hanyar daba masa wuka mai kaifin gaske a ciki da kuma hannu, bayan ya kai masa hari a lokacin bikin murnar zagayowar ranar samun ‘yancin kai tare da karbar wayarsa ta Samsung.
Mai gabatar da kara ya gabatar da shaidu biyar, domin tabbatar da tuhumar da ake yi wa wanda ake tuhumar.
Sai dai, mai laifin ya musanta aikata laifin. A cewar mai gabatar da kara, laifin ya ci karo da tanadin sashe na 298 da 221 na kundin laifuffuka.















Discussion about this post