ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Kan Ƙoƙarin Rage Farashin Takin Zamani — Ƙungiyar FEPSAN

by Abubakar Abba
6 months ago
Farashin

Shugaban kungiyar masu sarrafa takin zamani da rabar da shi na kasa (FEPSAN), Injiya Olusegun Falade ya bayyana cewa; kungiyar na kan koarin ganin an rage tsadar farashinsa.

Ya sanar da haka ne a Jihar Kaduna, a taron wayar da kai na tababatar da sahihancin takin zamanin na samarin NPK da cibiyar kasa da bunkasa samar da takin zamni (IFDC), ta dauki nauyi na 2025.

  • Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas
  • Matatar Dangote Ta Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 699

“Na kasance daga cikin wadanda suke kan gaba wajen ganin shirin ya dore, hakan zai bayar da dama domin ganin kowa ya samu alkaluman da ake bukata a bangaren samar da bayanai, musamman a fannin masana’antar sarrafa takin zamani,” a cewar shugaban.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, ba wai taki ba ne kadai farashinsa ya tashi, hatta kusan komai farashinsa ya karu a Nijeriya, musamman a cikin shekaru biyu da suka gabata.

Shugaban ya ci gaba da cewa, manyan dalilai biyu ne kusan suka sanya farashin ya tashi a kasar nan, musamman sabbin sauye-sauyen da gwamnatin tarayya ta kirkiro da kuma rashin samun tabbacin farashin kaya a kasuwannin kasar, wanda hakan ya jawo mutane suke daukar matakan da ba su dace ba.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Ya yi nuni da cewa, sakamakon yakin da ake ci gaba da gabzawa a tsakanin Kasahen Russia da Ukraine, tun a 2022, hakan ya haifar da tashin farashinsa a daukacin fadin duniya.

Shugaban ya kara da cewa, hatta farashin sinadarin hada takin na MOP, wato Potash ya tashi, haka farashin sinadarin DAP, wato Diammonium Phosphate shi ma ya tashin zuwa sama da dala 900 kan tan ko sama da dala 1,000, a wasu lokutan, inda a yanzu ya kai dala 700 kowane tan daya.

Ya sanar da cewa, idan mutane sun koka kan tashin farashinsa, mu ma muna jaddada musu cewa, mun saye shi da tsada, wanda kuma idan farashin dala ya tashi a duniya, hakan na shafar farashin naira.

Sai dai, ya bayyana cewa; kungiyar na ci gaba da gudanar da rabon takin, ba tare da an kara masa wani farashi mai tsada ba, inda yayi nuni da cewa, ba don samar da wannan dauki ba, da yanzu farashinsa ya karu.

A cewarsa, mun tattauna da kwamitin da ke samar da daidaiton farashinsa tare da hadaka da hukumar zuba jari ta kasa (NSIA) da kuma taimakawar sashen kudi MOFI, na ma’aikatar kudi ta tarayya, wadanda ya sanar da cewa; suna kan kokarinsu wajen ganin an samar da sauki kan farashinsa.

Ko da yake, ba a lokaci guda za a wanzar da hakan ba, amma muna sa ran a 2026, farashin zai ragu.

Ya kara da cewa, ana kuma ci gaba da samun raguwar farashin kayan da ake hada takin zamanin da su.

Ya ci gada cewa, gwamnatin tarayya na ci gaba da kokarin daidaita farashin kayan da ake sarrafa takin zamani, wanda hakan zai bayar da damar gudanar da gasa a kasuwar da ake sayar da shi, wanda kuma har yanzu, ana ci gaba da yin wannan tsari.

Ya sanar da cewa, har zuwa yanzu, muna ci gaba da tabbatar da cewa; farashin nasa ya ragu.

Kan batun baragurbin da ke gurbata takin, shugaban ya sanar da cewa; kasancewarmu a kan gaba wajen sarrafa takin a kasar nan, gurbata takin na daga cikin matsalar da ke shafar mu.

A cewarsa, irin wadannan bata gari na kwaikwayar buhunhunan da muke zuba taki tare da sayar wa jama’a.

“Idan mun gano, muna kama irin wadannan bata gari ko kuma mu kore su daga kasuwar, a yanzu muna yin amfani da kimiyyar fasahar zamani wajen yakar masu gurbata takin, in ji shugaban.

Farashin
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Farashin

Matakan Dauda Lawal Na Samar Da Tsaro A Zamfara: An Bankado Ayyukan Masu Zagon Ƙasa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.