ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matakan Dauda Lawal Na Samar Da Tsaro A Zamfara: An Bankado Ayyukan Masu Zagon Ƙasa

by Bello Hamza
6 months ago
Dauda

Adaidai lokacin da matsalar tsaro ke kara rinchabewa a wasu sassan kaasar nan, wasu jihohi na matukar kokarin su na ganin an shawo kan matsalar a yankunan su. Masu lura da al’amurran yau da kullum sun tabbatar da cewa, an samu nasarori masu yawa a kokarin da Gwamnan Jihar Zamfara yake yi domin ganin jihar ta kawo karshen ayyukan ‘yan bindiga, kuma daga dukkan alamu ana samu nasara. Matakan Gwamna Dauda Lawal suna haifar da da mai ido.

Sai dai kuma abin takaici a daidai wannan lokacin shi ne yadda wasu marasa kishin kasa wadanda basu yi wa al’umma Jihar Zamfara da Nijeriya fatan alhairi suke amfani da wasu kungiyoyin boyi wajen yada labarun kanzon kurege don yin zagon kasa ga kokarin da Gwamna Lawal ke yi.

  • Tinubu Na Ɗaukar Ƙwararan Matakai Don Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya – Shettima
  • Binciken CGTN: Ya Kamata A Dauki Matakai Don Kula Da Yanayin Duniya

An gano cewa zargin da ake yadawa cewa Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi afuwa tare da sakin ‘yan bindiga da aka yanke wa hukunci ba shi da tushe kwata-kwata, bayan cikakken bincike da jaridar PremiumTimes ta gudanar kan batun da ya tayar da kura a kafafen yada labarai.

ADVERTISEMENT

A ranar 28 ga Nuwamban 2025, wata kungiya mai suna ‘Human Rights Watchdog in Africa’ (HRWA) ta fitar da wata sanarwa da aka ce daraktanta, Samson Adamu, ne ya sanya wa hannu, inda ta bukaci Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, da ya ayyana dokar ta-baci a Zamfara, bisa zargin cewa Gwamna Lawal ya yi afuwa tare da sakin ’yan bindiga 69 ta sirri, karkashin wani shiri da ta kira ‘Religious Amnesty.’

Sai dai binciken da aka gudanar ya nuna cewa ba a samu asalin wannan sanarwa daga kowace sahihiyar majiya ba. Kokarin samun kungiyar HRWA da shugabanta Samson Adamu ya ci tura, domin babu wani ofishinta, lambar waya, shafin yanar gizo ko kuma rajistarta da aka samu a Hukumar Kula da Kamfanoni da Kungiyoyi ta Kasa. Haka nan, babu wani sahihin bayani ko sahihiyar shaidar da ke nuna wanzuwar kungiyar ko wannan mutum kafin karshen Nuwamban 2025.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Bincike ya kuma tabbatar da cewa abin da ya faru a zahiri shi ne Hukumar Zakka da Wakafi ta Jihar Zamfara ta taimaka wajen biyan basussukan fursunonin da aka yanke wa hukunci a shari’o’in farar hula, wanda hakan ya taimaka wajen sakin mutum 909 daga 2024 zuwa 2025. Wannan bayani ya fito ne daga bakin Sakataren Zartarwa na hukumar, Habib Muhammad Balarabe, a wani taron karshen shekara da aka gudanar a Gusau.

A cewarsa, a 2024 kadai, an biya basussukan fursunoni 473, yayin da a 2025 aka kashe Naira miliyan 67.2 domin biyan basussukan mutum 436, wanda adadin gaba daya ya kai 909 cikin shekaru biyu. Hukumar ta kuma bayar da tallafin jari ga mata 200 kanana ‘yan kasuwa da Naira dubu 50-50, tare da bai wa wasu mata 100 kayan fara sana’a bayan kammala horarwar kiwon kaji na makonni uku.

Jami’an hukumar Zakka sun bayyana cewa ayyukansu na jinkai ba su taba shafar ‘yan bindiga da aka yanke wa hukunci kan laifukan ta’addanci ba. Wani jami’i da ya nemi a sakaya sunansa ya ce, abin dariya ne ace gwamnan da ya sha bayyana a fili cewa ba ya sulhu da ‘yan bindiga shi ne zai koma ya sake su bayan an yanke musu hukunci.

Haka kuma, an tabbatar da cewa Gwamna Lawal bai taba sauya matsayarsa kan batun ‘yan bindiga ba. A ranar 29 ga Oktoban 2025, yayin da yake jawabi a gaban daliban kwas din tsaro a ‘National Institute for Security Studies’ da ke Abuja, gwamnan ya bayyana adawarsa ga yarjejeniyar sulhu da ‘yan bindiga da ake yi a wasu jihohin Arewa maso Yamma, yana mai cewa sulhu ba tare da kwace makamai ba hanya ce ta jinkirta tashin hankali.

Kakakin gwamnan, Suleman Bala Idris, ya musanta zargin baki daya, yana mai cewa labarin kirkirarre ne da wasu ‘yan siyasa da ke cikin matsin lamba suka tsara domin bata sunan gwamnatin Zamfara.

Ya jaddada cewa babu wani lokaci da Gwamna Lawal ya yi afuwa ko ya saki kowane dan bindiga daga kurkuku.

Bayan kammala bincike mai zurfi, an tabbatar da cewa kungiyar HRWA da shugaban nata kamar fatalwa ne, kuma zargin da aka yi cewa Gwamna Lawal ya saki ‘yan bindiga karya ne tsagwaron gaske.

Dauda
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
EU Ta Koka Da Yadda Yaduwar Ta’addanci A Sahel Ke Barazana Ga Tsaron Turai

EU Ta Koka Da Yadda Yaduwar Ta'addanci A Sahel Ke Barazana Ga Tsaron Turai

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.