Mustapha Sule Lamido, ɗan tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido, ya zama ɗan takarar gwamna na jam’iyyar PDP domin zaɓen 2027 bayan samun amincewa yayin zaman sulhu daga dukkan ƙananan hukumomi 27 na jihar.
Shugaban kwamitin zaɓen da shalƙwatar PDP ta kafa, Isah Ahmed, ya sanar da fitowar Lamido ba tare da hamayya ba, yana mai cewa duk sauran masu neman takarar sun janye. Ya bayyana cewa wakilai daga sassan jihar sun tabbatar da takararsa ta hanyar kaɗa ƙuri’ar cikin lumana da bin tsarin dimokuraɗiyyar jam’iyyar.
Shugaban PDP na jihar Jigawa, Babandi Ibrahim, ya taya Lamido da magoya bayan jam’iyyar murna, yana mai yabawa yadda aka gudanar da zaɓen fidda gwanin cikin kwanciyar hankali da haɗin kai.
A jawabin karɓar takarar, Mustapha Sule Lamido ya bayyana nasarar tasa a matsayin kira zuwa yin hidima da kuma damar ceto jihar daga matsin tattalin arziƙi da rashin shugabanci mai inganci.
Lamido ya yi alƙawarin mayar da hankali kan bunƙasa matasa, da ilimi, da lafiya, da ci gaban tattalin arziƙi da gyaran cibiyoyin gwamnati idan aka zaɓe shi gwamna a 2027, tare da kira ga ‘yan PDP da su ci gaba da haɗa kai domin cimma nasara a babban zaɓe mai zuwa.















Discussion about this post