ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 weeks ago
Children waves flowers and American and Chinese flags before President Donald Trump is greeted by Chinese President Xi Jinping at a welcome ceremony at the Great Hall of the People, Thursday, May 14, 2026, in Beijing. (AP Photo/Mark Schiefelbein)

Children waves flowers and American and Chinese flags before President Donald Trump is greeted by Chinese President Xi Jinping at a welcome ceremony at the Great Hall of the People, Thursday, May 14, 2026, in Beijing. (AP Photo/Mark Schiefelbein)

A cikin watanni 6 da suka gabata, shugabannin kasashen da ke da kujerun dindindin a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, da na kasashe mambobin kungiyar kasashe 7 masu karfin masana’antu ta G7, kusan dukkansu sun kawo ziyara kasar Sin daya bayan daya.

Dangane da batun, shahararren dan jarida na kasar Zimbabwe, Mabasa Sasa, ya rubuta wani bayani, wanda aka nuna shi a shafin yanar gizo na jaridar “The Herald” ta kasar Zimbabwe, inda ya ce, jami’ai da kafofin yada labarai na kasashen yamma su kan yi kokarin saka ra’ayin rashin amincewa da kasar Sin cikin zukatan mutanen Afirka, a yayin da su da kansu suke ta kokarin karfafa hadin gwiwa tare da kasar Sin.

Mista Sasa ya ce, ya kamata kasashen Afirka su magance fadawa cikin tarkon tunani da aka haka musu, kuma su kara zurfafa hadin gwiwa da kasar Sin.Sa’an nan, a nasa bangare, wani shehun malami dan Najeriya mai suna Olalekan Babatunde, a cikin makalarsa da aka buga a jaridar “The Nation” ta kasar Najeriya, ya ce babban dalilin da ya janyo shugabannin kasashe daban daban zuwa ziyara a kasar Sin, shi ne muhimmin matsayin da kasar Sin ke da shi a duniya, a fannonin tattalin arziki, da diflomasiyya, da kimiyya da fasaha, da tsare-tsaren raya kasa. Kana ya shawarci kasashen Afirka da su yi amfani da damammakin da kasar Sin ta samar, a kokarin raya tattalin arzikinsu.

ADVERTISEMENT

Hakika, akwai abubuwa da dama da suka janyo hankalin shugabannin kasashe daban daban don ziyartar kasar Sin, wadanda suka hada da matsayin kasar Sin mai muhimmanci a duniya, gami da wasu manyan manufofi na kasar.Da farko, tsarin tattalin arziki na gurguzu mai salon musamman na Sin ya tabbatar da yanayin ci gaban tattalin arzikin kasar cikin sauri.

Wannan tsari ya ba gwamnati damar samar da jagoranci mai karfi, da baiwa kamfanoni masu zaman kansu damar raya kansu bisa shirin raya kasa na dogon lokaci da gwamnati ta tsara. Saboda haka, a lokacin da bangarorin kasashe daban daban ke hulda da kasar Sin, suna hulda da wata babbar kasuwa, inda ake samun manufofi masu tabbaci, da makomar karuwa mai dorewa.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Na biyu shi ne, yadda kasar Sin ke tsayawa tsayin daka kan raya kasa ta hanyar lumana. A lokacin da kasar Sin ke hulda da sauran kasashe, ba ta son ganin taho-mu-gama da ake yi tsakanin rukunoni daban daban, wadanda suke da bambancin ra’ayi. Maimakon haka, kasar Sin na son karfafa cudanya da hadin gwiwa tsakanin mabambantan al’ummu, ta yadda za a iya tabbatar da moriyar dukkansu.

Kana na uku shi ne, ra’ayin kasar Sin na gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya.Bisa wannan ra’ayi ne, kasar Sin ta gabatar da shirin “Ziri Daya da Hanya Daya”, da shawarwari masu nasaba da harkokin raya kasa, da tsaro, da cudanyar al’adu, da kula da al’amuran duniya.

Ban da haka, kasar na son raba moriya tare da sauran kasashe, wanda ya zama dalilin da ya sa ta aiwatar da hadin gwiwa da kasashen dukkan nahiyoyin Asiya, da Turai, da Afirka, da Latin Amurka, bisa shirin “Ziri Daya da Hanya Daya”, da yafe wa kasashe 53 dake nahiyar Afirka da suka kulla huldar diflomasiyya da ita harajin fito, da dai sauransu.

A takaice dai, manufofin kasar Sin sun sa kasashe daban daban fahimtar cewa, hadin gwiwa tare da ita zai samar musu da kyakkyawar damar raya kai, da samun kwanciyar hankali, da zama masu walwala tare. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa
  • Sulaiman
    Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass
  • Sulaiman
    Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Ƴan Majalisar Dokokin Ƙasa 54 Sun Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fidda Gwanin APC

Ƴan Majalisar Dokokin Ƙasa 54 Sun Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fidda Gwanin APC

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

June 26, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A  Titin Bypass

Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass

June 26, 2026
Disu

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

June 26, 2026
Sin

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fara Aikin Gina Mayankar Zamani A Garin Jos

June 26, 2026
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

June 26, 2026
NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ba Ta Da Hujjar Umartar INEC Ta Soke Rajistar Jam’iyyu —Uban Doman Lafiya

June 26, 2026
Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.