ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
Children waves flowers and American and Chinese flags before President Donald Trump is greeted by Chinese President Xi Jinping at a welcome ceremony at the Great Hall of the People, Thursday, May 14, 2026, in Beijing. (AP Photo/Mark Schiefelbein)

Children waves flowers and American and Chinese flags before President Donald Trump is greeted by Chinese President Xi Jinping at a welcome ceremony at the Great Hall of the People, Thursday, May 14, 2026, in Beijing. (AP Photo/Mark Schiefelbein)

A cikin watanni 6 da suka gabata, shugabannin kasashen da ke da kujerun dindindin a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, da na kasashe mambobin kungiyar kasashe 7 masu karfin masana’antu ta G7, kusan dukkansu sun kawo ziyara kasar Sin daya bayan daya.

Dangane da batun, shahararren dan jarida na kasar Zimbabwe, Mabasa Sasa, ya rubuta wani bayani, wanda aka nuna shi a shafin yanar gizo na jaridar “The Herald” ta kasar Zimbabwe, inda ya ce, jami’ai da kafofin yada labarai na kasashen yamma su kan yi kokarin saka ra’ayin rashin amincewa da kasar Sin cikin zukatan mutanen Afirka, a yayin da su da kansu suke ta kokarin karfafa hadin gwiwa tare da kasar Sin.

Mista Sasa ya ce, ya kamata kasashen Afirka su magance fadawa cikin tarkon tunani da aka haka musu, kuma su kara zurfafa hadin gwiwa da kasar Sin.Sa’an nan, a nasa bangare, wani shehun malami dan Najeriya mai suna Olalekan Babatunde, a cikin makalarsa da aka buga a jaridar “The Nation” ta kasar Najeriya, ya ce babban dalilin da ya janyo shugabannin kasashe daban daban zuwa ziyara a kasar Sin, shi ne muhimmin matsayin da kasar Sin ke da shi a duniya, a fannonin tattalin arziki, da diflomasiyya, da kimiyya da fasaha, da tsare-tsaren raya kasa. Kana ya shawarci kasashen Afirka da su yi amfani da damammakin da kasar Sin ta samar, a kokarin raya tattalin arzikinsu.

ADVERTISEMENT

Hakika, akwai abubuwa da dama da suka janyo hankalin shugabannin kasashe daban daban don ziyartar kasar Sin, wadanda suka hada da matsayin kasar Sin mai muhimmanci a duniya, gami da wasu manyan manufofi na kasar.Da farko, tsarin tattalin arziki na gurguzu mai salon musamman na Sin ya tabbatar da yanayin ci gaban tattalin arzikin kasar cikin sauri.

Wannan tsari ya ba gwamnati damar samar da jagoranci mai karfi, da baiwa kamfanoni masu zaman kansu damar raya kansu bisa shirin raya kasa na dogon lokaci da gwamnati ta tsara. Saboda haka, a lokacin da bangarorin kasashe daban daban ke hulda da kasar Sin, suna hulda da wata babbar kasuwa, inda ake samun manufofi masu tabbaci, da makomar karuwa mai dorewa.

LABARAI MASU NASABA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Na biyu shi ne, yadda kasar Sin ke tsayawa tsayin daka kan raya kasa ta hanyar lumana. A lokacin da kasar Sin ke hulda da sauran kasashe, ba ta son ganin taho-mu-gama da ake yi tsakanin rukunoni daban daban, wadanda suke da bambancin ra’ayi. Maimakon haka, kasar Sin na son karfafa cudanya da hadin gwiwa tsakanin mabambantan al’ummu, ta yadda za a iya tabbatar da moriyar dukkansu.

Kana na uku shi ne, ra’ayin kasar Sin na gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya.Bisa wannan ra’ayi ne, kasar Sin ta gabatar da shirin “Ziri Daya da Hanya Daya”, da shawarwari masu nasaba da harkokin raya kasa, da tsaro, da cudanyar al’adu, da kula da al’amuran duniya.

Ban da haka, kasar na son raba moriya tare da sauran kasashe, wanda ya zama dalilin da ya sa ta aiwatar da hadin gwiwa da kasashen dukkan nahiyoyin Asiya, da Turai, da Afirka, da Latin Amurka, bisa shirin “Ziri Daya da Hanya Daya”, da yafe wa kasashe 53 dake nahiyar Afirka da suka kulla huldar diflomasiyya da ita harajin fito, da dai sauransu.

A takaice dai, manufofin kasar Sin sun sa kasashe daban daban fahimtar cewa, hadin gwiwa tare da ita zai samar musu da kyakkyawar damar raya kai, da samun kwanciyar hankali, da zama masu walwala tare. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK
  • Sulaiman
    Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA
  • Sulaiman
    Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti
  • Sulaiman
    Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

MASU ALAKA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Next Post
Ƴan Majalisar Dokokin Ƙasa 54 Sun Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fidda Gwanin APC

Ƴan Majalisar Dokokin Ƙasa 54 Sun Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fidda Gwanin APC

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026
Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.