A cikin watanni 6 da suka gabata, shugabannin kasashen da ke da kujerun dindindin a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, da na kasashe mambobin kungiyar kasashe 7 masu karfin masana’antu ta G7, kusan dukkansu sun kawo ziyara kasar Sin daya bayan daya.
Dangane da batun, shahararren dan jarida na kasar Zimbabwe, Mabasa Sasa, ya rubuta wani bayani, wanda aka nuna shi a shafin yanar gizo na jaridar “The Herald” ta kasar Zimbabwe, inda ya ce, jami’ai da kafofin yada labarai na kasashen yamma su kan yi kokarin saka ra’ayin rashin amincewa da kasar Sin cikin zukatan mutanen Afirka, a yayin da su da kansu suke ta kokarin karfafa hadin gwiwa tare da kasar Sin.
Mista Sasa ya ce, ya kamata kasashen Afirka su magance fadawa cikin tarkon tunani da aka haka musu, kuma su kara zurfafa hadin gwiwa da kasar Sin.Sa’an nan, a nasa bangare, wani shehun malami dan Najeriya mai suna Olalekan Babatunde, a cikin makalarsa da aka buga a jaridar “The Nation” ta kasar Najeriya, ya ce babban dalilin da ya janyo shugabannin kasashe daban daban zuwa ziyara a kasar Sin, shi ne muhimmin matsayin da kasar Sin ke da shi a duniya, a fannonin tattalin arziki, da diflomasiyya, da kimiyya da fasaha, da tsare-tsaren raya kasa. Kana ya shawarci kasashen Afirka da su yi amfani da damammakin da kasar Sin ta samar, a kokarin raya tattalin arzikinsu.
Hakika, akwai abubuwa da dama da suka janyo hankalin shugabannin kasashe daban daban don ziyartar kasar Sin, wadanda suka hada da matsayin kasar Sin mai muhimmanci a duniya, gami da wasu manyan manufofi na kasar.Da farko, tsarin tattalin arziki na gurguzu mai salon musamman na Sin ya tabbatar da yanayin ci gaban tattalin arzikin kasar cikin sauri.
Wannan tsari ya ba gwamnati damar samar da jagoranci mai karfi, da baiwa kamfanoni masu zaman kansu damar raya kansu bisa shirin raya kasa na dogon lokaci da gwamnati ta tsara. Saboda haka, a lokacin da bangarorin kasashe daban daban ke hulda da kasar Sin, suna hulda da wata babbar kasuwa, inda ake samun manufofi masu tabbaci, da makomar karuwa mai dorewa.
Na biyu shi ne, yadda kasar Sin ke tsayawa tsayin daka kan raya kasa ta hanyar lumana. A lokacin da kasar Sin ke hulda da sauran kasashe, ba ta son ganin taho-mu-gama da ake yi tsakanin rukunoni daban daban, wadanda suke da bambancin ra’ayi. Maimakon haka, kasar Sin na son karfafa cudanya da hadin gwiwa tsakanin mabambantan al’ummu, ta yadda za a iya tabbatar da moriyar dukkansu.
Kana na uku shi ne, ra’ayin kasar Sin na gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya.Bisa wannan ra’ayi ne, kasar Sin ta gabatar da shirin “Ziri Daya da Hanya Daya”, da shawarwari masu nasaba da harkokin raya kasa, da tsaro, da cudanyar al’adu, da kula da al’amuran duniya.
Ban da haka, kasar na son raba moriya tare da sauran kasashe, wanda ya zama dalilin da ya sa ta aiwatar da hadin gwiwa da kasashen dukkan nahiyoyin Asiya, da Turai, da Afirka, da Latin Amurka, bisa shirin “Ziri Daya da Hanya Daya”, da yafe wa kasashe 53 dake nahiyar Afirka da suka kulla huldar diflomasiyya da ita harajin fito, da dai sauransu.
A takaice dai, manufofin kasar Sin sun sa kasashe daban daban fahimtar cewa, hadin gwiwa tare da ita zai samar musu da kyakkyawar damar raya kai, da samun kwanciyar hankali, da zama masu walwala tare. (Bello Wang)















Discussion about this post