ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 days ago
Children waves flowers and American and Chinese flags before President Donald Trump is greeted by Chinese President Xi Jinping at a welcome ceremony at the Great Hall of the People, Thursday, May 14, 2026, in Beijing. (AP Photo/Mark Schiefelbein)

Children waves flowers and American and Chinese flags before President Donald Trump is greeted by Chinese President Xi Jinping at a welcome ceremony at the Great Hall of the People, Thursday, May 14, 2026, in Beijing. (AP Photo/Mark Schiefelbein)

A cikin watanni 6 da suka gabata, shugabannin kasashen da ke da kujerun dindindin a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, da na kasashe mambobin kungiyar kasashe 7 masu karfin masana’antu ta G7, kusan dukkansu sun kawo ziyara kasar Sin daya bayan daya.

Dangane da batun, shahararren dan jarida na kasar Zimbabwe, Mabasa Sasa, ya rubuta wani bayani, wanda aka nuna shi a shafin yanar gizo na jaridar “The Herald” ta kasar Zimbabwe, inda ya ce, jami’ai da kafofin yada labarai na kasashen yamma su kan yi kokarin saka ra’ayin rashin amincewa da kasar Sin cikin zukatan mutanen Afirka, a yayin da su da kansu suke ta kokarin karfafa hadin gwiwa tare da kasar Sin.

Mista Sasa ya ce, ya kamata kasashen Afirka su magance fadawa cikin tarkon tunani da aka haka musu, kuma su kara zurfafa hadin gwiwa da kasar Sin.Sa’an nan, a nasa bangare, wani shehun malami dan Najeriya mai suna Olalekan Babatunde, a cikin makalarsa da aka buga a jaridar “The Nation” ta kasar Najeriya, ya ce babban dalilin da ya janyo shugabannin kasashe daban daban zuwa ziyara a kasar Sin, shi ne muhimmin matsayin da kasar Sin ke da shi a duniya, a fannonin tattalin arziki, da diflomasiyya, da kimiyya da fasaha, da tsare-tsaren raya kasa. Kana ya shawarci kasashen Afirka da su yi amfani da damammakin da kasar Sin ta samar, a kokarin raya tattalin arzikinsu.

ADVERTISEMENT

Hakika, akwai abubuwa da dama da suka janyo hankalin shugabannin kasashe daban daban don ziyartar kasar Sin, wadanda suka hada da matsayin kasar Sin mai muhimmanci a duniya, gami da wasu manyan manufofi na kasar.Da farko, tsarin tattalin arziki na gurguzu mai salon musamman na Sin ya tabbatar da yanayin ci gaban tattalin arzikin kasar cikin sauri.

Wannan tsari ya ba gwamnati damar samar da jagoranci mai karfi, da baiwa kamfanoni masu zaman kansu damar raya kansu bisa shirin raya kasa na dogon lokaci da gwamnati ta tsara. Saboda haka, a lokacin da bangarorin kasashe daban daban ke hulda da kasar Sin, suna hulda da wata babbar kasuwa, inda ake samun manufofi masu tabbaci, da makomar karuwa mai dorewa.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Na biyu shi ne, yadda kasar Sin ke tsayawa tsayin daka kan raya kasa ta hanyar lumana. A lokacin da kasar Sin ke hulda da sauran kasashe, ba ta son ganin taho-mu-gama da ake yi tsakanin rukunoni daban daban, wadanda suke da bambancin ra’ayi. Maimakon haka, kasar Sin na son karfafa cudanya da hadin gwiwa tsakanin mabambantan al’ummu, ta yadda za a iya tabbatar da moriyar dukkansu.

Kana na uku shi ne, ra’ayin kasar Sin na gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya.Bisa wannan ra’ayi ne, kasar Sin ta gabatar da shirin “Ziri Daya da Hanya Daya”, da shawarwari masu nasaba da harkokin raya kasa, da tsaro, da cudanyar al’adu, da kula da al’amuran duniya.

Ban da haka, kasar na son raba moriya tare da sauran kasashe, wanda ya zama dalilin da ya sa ta aiwatar da hadin gwiwa da kasashen dukkan nahiyoyin Asiya, da Turai, da Afirka, da Latin Amurka, bisa shirin “Ziri Daya da Hanya Daya”, da yafe wa kasashe 53 dake nahiyar Afirka da suka kulla huldar diflomasiyya da ita harajin fito, da dai sauransu.

A takaice dai, manufofin kasar Sin sun sa kasashe daban daban fahimtar cewa, hadin gwiwa tare da ita zai samar musu da kyakkyawar damar raya kai, da samun kwanciyar hankali, da zama masu walwala tare. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
τ-Law Ya Nuna Jajircewar Kasar Sin
Ra'ayi Riga

τ-Law Ya Nuna Jajircewar Kasar Sin

May 27, 2026
Next Post
Ƴan Majalisar Dokokin Ƙasa 54 Sun Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fidda Gwanin APC

Ƴan Majalisar Dokokin Ƙasa 54 Sun Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fidda Gwanin APC

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.