Aƙalla ƴan majalisar dokokin ƙasa 54 masu ci ne suka rasa tikitin sake neman zaɓe a majalisar dokoki ta ƙasa a zaɓen fidda gwani na jam’iyyar APC.
Jam’iyyar APC ta gudanar da zaɓen fidda gwani na majalisar wakilai a ranar Asabar, 16 ga Mayu, yayin da na sanatoci ya gudana ranar Litinin, 18 ga Mayu, 2026.
Daga cikin waɗanda suka sha kaye akwai fitattun ƴan majalisa da suka kwashe shekaru masu yawa a majalisar dokoki ta ƙasa, yayin da wasu kuma manyan jami’ai ne a majalisar wakilai da majalisar dattawa.
A majalisar wakilai, waɗanda suka rasa tikitin sun haɗa da Hon. Nicholas Mutu mai wakiltar mazaɓar Bomadi/Patani ta Jihar Delta; shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai, Farfesa Julius Ihonɓbere mai wakiltar mazaɓar Owan ta Jihar Edo; Ibrahim Isiaka mai wakiltar Ifo/Ewekoro a Jihar Ogun; da Mike Etaba mai wakiltar Obubra/Etung a Jihar Cross Riɓer.
Sauran sun haɗa da Ngozi Lawrence Okolie (Aniocha/Oshimili, Delta); Daɓid Zachariya (Igalamela/Idah, Kogi); Tijani Ahmed Ozigi (Okene/Ogori-Magongo, Kogi); Eseosa Iyawe (Oredo, Edo); Matthew Nwogu (Aboh Mbaise/Ngor Okpala, Imo); Miriam Onuoha (Okigwe North, Imo); da Chike Okafor (Okigwe South, Imo).
Waɗanda su ma suka rasa tikitinsu kuma ba za su dawo majalisar dokoki ta ƙasa ba sun haɗa da; Harrison Nwadike (Isu/Njaba/Nkwerre/Nwangele, Imo); Emeka Martins Chinedu (Ahiazu/Ezinihitte, Imo); Ismail Kayode (Ifelodun/Oyun/Offa, Kwara); Mansur Musa Jega (Jega/Gwandu/Aleiro, Kebbi); Muktar Muhammad (Kazaure/Roni/Gwiwa Yankwashi, Jigawa); da Ibrahim Usman Auyo (Hadejia/Auyo/Kafin Hausa, Jigawa).
Hakazalika, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazaɓar Ringim/Taura ta Jihar Jigawa, Hon. Sa’adu Wada Taura, ya rasa tikitin tsayawa takara a zaɓen 2027 bayan da Yushau Muhammad ya samu tikitin ta hanyar maslaha.
Sauran da ba za su koma majalisar wakilai ba sun haɗa da Yusif Sa’idu Miga (Jahun/Miga, Jigawa); Dickson Tarkighir (Makurdi/Guma, Benuwe); Terseer Ugbor (Kwande/Ushongo, Benuwe); Sesoo Ikpagher (Ɓandeikya/Konshisha, Benuwe); Asema Achado (Gwer East/Gwer West, Benuwe); Sekaɓ Iortyom (Buruku, Benuwe); Daɓid Ogewu (Oju/Obi, Benuwe); Bassey Akiba (Odukpani/Calabar Municipality, Cross Riɓer); da Daniel Asama (Jos North/Bassa, Plateau).
A zaɓen fidda gwani mai zafi, Ɓincent Bulus (Langtang, Filato); John Dafaan (Ƙua’anpan/Shendam/Mikang, Plateau); Ajang Iliya (Jos South/Jos East, Plateau); Jeremiah Umaru (Wamba/Akwanga/Nasarawa Eggon); Ari Mohamed Abdul-Mumin (Nasarawa/Toto); Abiodun Akinlade (Ipokia/Yewa South, Ogun); da Tunji Akinosi (Ado-Odo/Ota, Ogun) su ma sun sha kaye.
Haka kuma, Femi Ogunbanwo (Odogbolu/Ijebu Ode/Ijebu North East, Ogun); Adesola Elegbeji (Remo, Ogun); da Jimi Odimayo (Okitipupa/Irele, Ondo) sababbin ƴan takara sun kayar da su a zaɓen fidda gwani.
Donatus Mathew, tsohon direban babur kasuwanci wanda ya lashe kujerar majalisar wakilai ta mazaɓar Kaura a Jihar Kaduna a ƙarƙashin jam’iyyar Labour Party a 2023 amma ya koma APC a Disambar 2024, ya rasa ƙoƙarinsa na komawa majalisar ta sabuwar jam’iyyarsa.
Haka kuma waɗanda aka kayar sun haɗa da Timilehin Adelegbe (Owo/Ose, Ondo); Bashiru Dawodu (Oshodi-Isolo, Lagos); Kafilat Ogbara (Kosofe, Lagos); da ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Ekiti North II, Akinlayo Kolawole, wanda ya rasa tikitin ga tsohon ɗan majalisar tarayya, Ibrahim Olarewaju.
A majalisar dattawa kuwa, waɗanda suka sha kaye sun haɗa da Ned Nwoko (Delta North), wanda tsohon gwamnan Jihar Delta, Ifeanyi Okowa, ya kayar; Neda Imasuen; Jibrin Isah mai wakiltar Kogi East wanda aka fi sani da Echocho; Sanata Muhammad Danjuma Goje wanda ya wakilci Gombe Central har sau huɗu a jere; da Sanata Adeniyi Adegbonmire (Ondo Central).
Sauran sun haɗa da Sanata Olajide Ipinsagba (Ondo North); Sanata Gbenga Daniel (Ogun East); Sanata Diket Plang (Plateau Central); Sanata Lola Ashiru (Kwara South); Sanata Emmanuel Udende wanda ya rasa tikitin Benuwe North East ga tsohon gwamnan Jihar, Sanata Gabriel Suswam; Sanata Titus Zam (Benuwe North West); da Sanata Olubiyi Fadeyi (Osun Central).















Discussion about this post