Rahotannin da aka ruwaito sun ce, tsohon ministan kudin kasar Girika, kana masanin tattalin arziki, Yanis Varoufakis, ya wallafa wani bayani a tashar intanet ta Project Syndicate, inda ya ce, kasashen yammacin duniya sun kitsa labaran bogi da ke cewa wai “kasar Sin ta samu ci gaba bisa dabarun yaudara” domin rufe asirin gazawarsu, don haka ya dace a kalli dalilin nasarar kasar Sin ta fannin tattalin arziki yadda ya kamata.
Game da wannan batu, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Mao Ning ta bayyana a yau Alhamis 9 ga wata cewa, nasarar da kasar ta samu ba ta faru kwatsam ba, akasin haka, ta shaida fa’idojin tsarin kasar, kana nasara ce da ta shafi turba da akida gami da salon kasar ta Sin. (Murtala Zhang)















Discussion about this post