Wani nazari da kafar CGTN ta wallafa a intanet ya nuna cewa, kaso 89.9 na masu bayar amsa a fadin duniya sun yi ammana cewa babu wata kasa da ya kamata ta yi biris da irin kalamai na baya-bayan nan da matakan da Japan ke aiwatarwa dake da nufin kawo tsaiko ga tsarin duniya bayan yakin duniya na II da dawo da ra’ayin amfani da karfin soji. Suna cewa, ya kamata kasa da kasa ciki har da Amurka, su hada hannu wajen bijirewa duk wani yunkuri na dawo da amfani da karfin soji.
An wallafa nazarin ne a dandalin CGTN na harsunan Ingilishi da Spaniyanci da Faransanci da Larabci da Rashanci, inda jimilar mutane 10,862 suka bayyana ra’ayoyinsa cikin sa’o’i 24. (Mai fassara: FMM)
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
ADVERTISEMENT














