ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Cafke Mai Juna Biyu, Uwa Mai Shayarwa Da Dalibar Jami’a Kan Safaran Miyagun Kwayoyi

by Khalid Idris Doya
4 years ago
NDLEA

Hukumar dakile safaran miyagun kwayoyi (NDLEA) ta cafke wata mata mai juna biyu da wata uwa mai jego da wata dalibar jami’a ‘yar aji biyu kan safaran miyagun kwayoyi.

Hukumar ta NDLEA ta ce, wadanda ake zargin su na daga cikin mutum 28 ne da ta kama da tabar Wiwi mai nauyin kilogiram 9,437.7 da tabulet din maganin opioids da sauran miyagun kwayoyi a samamen da ta gudanar a jihohin 12 da suka kunshi: Yobe, Ondo, Edo, Rivers, Akwa Ibom, Imo, Jigawa, Kogi, Adamawa, Kaduna, Kwara, Lagos da kuma babban birnin tarayya Abuja.

  • NDLEA Ta Cafke Ƙwayar Tramadol Miliyan 13 Boye Cikin Wani Gida A Legas

Kakakin hukumar ta NDLEA, Femi Babafemi a FCT, ya ce, dakarunsu a ranar Asabar 15 ga watan Oktoba sun mamayi wani kauye mai suna Chukuku, mai nisan kilomita 10 da Gwagwalada inda suka gano wani katafaren rumbun boye tabar Wiwi.

ADVERTISEMENT

Inda aka kamo jumbo 510 na haramtattun tabar masu nauyin kilogiram 5, 640 tare da cafke wata mata mai shayarwa Sa’adatu Abdullahi, ‘yar shekara 35, da take kula da rumbun.

A jihar Yobe kuwa hukumar ta kama kilograms na tabar Wiwi 48 a Buni Yadi, kuma sun mamayi wani wuri da ke Potiskum inda suka kamo kilograms na tabar 31 daga wajen mutum biyu da ake zargi Mohammed Mamuda da wata matar aure mai juna biyu, Hauwa Haruna.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Kazalika, wata dalibin jami’ar karatu daga gida (NOUN) da ke karanta ilimin aikin jarida, Ms. Mercy Nyong, ‘yar shekara 30 a duniya, a ranar Laraba 12 ga watan Oktaba.ne ta fada tarkon hukumar a filin sauka da tashi na Jirgin saman kasa da kasa ta Murtala Muhammad da ke Ikeja, Legas a kokarinta na fita da garam 300 na Tramadol samfurin 225mg cikin abun boye turare zuwa Dubai.

Sannan wasu ‘yan kasar Ghana su 9 an cafke su a kokarinsu na yin safaran kilograms 10,843.95 na tabar Wiwi ta tekun Nijeriya, inda kuma a ranar Juma’a 14 ga watan Oktoba aka yanke musu hukuncin zaman gidan yari na shekara 72.

Da fari dai jami’an hukumar tsaron farin kaya ta NSCDC ne suka kama su kana suka mikasu ga hukumar NDLEA domin fadada bincike da gurfanar da su.

A karshe dai an gurfanar da su a kotu kan kara mai lamba FHC/L/292C/2021.

Da yake yanke hukunci a ranar Juma’a, Mai Shari’a Akintayo Aluko na babban kotun tarayya da ke Legas ya kama tare da daure ‘yan Ghana din bisa safaran Wiwi inda ya daure kowannesu shekara takwas a gidan yari.

Wadanda aka dauren su ne: Victor Wuddah; Freeman Gazul; Adotete Joseph; Sottie Moses; Sottie Stephen; Christian Tette; Kanu Okonipa; Daniel Koyepti; da Kanu Natte.

NDLEA
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

MASU ALAKA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027
Labarai

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
NDLEA Ta Cafke Mai Juna Biyu, Uwa Mai Shayarwa Da Dalibar Jami’a Kan Safaran Miyagun Kwayoyi

NDLEA Ta Cafke Mai Juna Biyu Da Dalibin Jami'a Kan Safarar Miyagun Kwayoyi

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.