ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Cafke Mai Juna Biyu, Uwa Mai Shayarwa Da Dalibar Jami’a Kan Safaran Miyagun Kwayoyi

by Khalid Idris Doya
4 years ago
NDLEA

Hukumar dakile safaran miyagun kwayoyi (NDLEA) ta cafke wata mata mai juna biyu da wata uwa mai jego da wata dalibar jami’a ‘yar aji biyu kan safaran miyagun kwayoyi.

Hukumar ta NDLEA ta ce, wadanda ake zargin su na daga cikin mutum 28 ne da ta kama da tabar Wiwi mai nauyin kilogiram 9,437.7 da tabulet din maganin opioids da sauran miyagun kwayoyi a samamen da ta gudanar a jihohin 12 da suka kunshi: Yobe, Ondo, Edo, Rivers, Akwa Ibom, Imo, Jigawa, Kogi, Adamawa, Kaduna, Kwara, Lagos da kuma babban birnin tarayya Abuja.

  • NDLEA Ta Cafke Ƙwayar Tramadol Miliyan 13 Boye Cikin Wani Gida A Legas

Kakakin hukumar ta NDLEA, Femi Babafemi a FCT, ya ce, dakarunsu a ranar Asabar 15 ga watan Oktoba sun mamayi wani kauye mai suna Chukuku, mai nisan kilomita 10 da Gwagwalada inda suka gano wani katafaren rumbun boye tabar Wiwi.

ADVERTISEMENT

Inda aka kamo jumbo 510 na haramtattun tabar masu nauyin kilogiram 5, 640 tare da cafke wata mata mai shayarwa Sa’adatu Abdullahi, ‘yar shekara 35, da take kula da rumbun.

A jihar Yobe kuwa hukumar ta kama kilograms na tabar Wiwi 48 a Buni Yadi, kuma sun mamayi wani wuri da ke Potiskum inda suka kamo kilograms na tabar 31 daga wajen mutum biyu da ake zargi Mohammed Mamuda da wata matar aure mai juna biyu, Hauwa Haruna.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Kazalika, wata dalibin jami’ar karatu daga gida (NOUN) da ke karanta ilimin aikin jarida, Ms. Mercy Nyong, ‘yar shekara 30 a duniya, a ranar Laraba 12 ga watan Oktaba.ne ta fada tarkon hukumar a filin sauka da tashi na Jirgin saman kasa da kasa ta Murtala Muhammad da ke Ikeja, Legas a kokarinta na fita da garam 300 na Tramadol samfurin 225mg cikin abun boye turare zuwa Dubai.

Sannan wasu ‘yan kasar Ghana su 9 an cafke su a kokarinsu na yin safaran kilograms 10,843.95 na tabar Wiwi ta tekun Nijeriya, inda kuma a ranar Juma’a 14 ga watan Oktoba aka yanke musu hukuncin zaman gidan yari na shekara 72.

Da fari dai jami’an hukumar tsaron farin kaya ta NSCDC ne suka kama su kana suka mikasu ga hukumar NDLEA domin fadada bincike da gurfanar da su.

A karshe dai an gurfanar da su a kotu kan kara mai lamba FHC/L/292C/2021.

Da yake yanke hukunci a ranar Juma’a, Mai Shari’a Akintayo Aluko na babban kotun tarayya da ke Legas ya kama tare da daure ‘yan Ghana din bisa safaran Wiwi inda ya daure kowannesu shekara takwas a gidan yari.

Wadanda aka dauren su ne: Victor Wuddah; Freeman Gazul; Adotete Joseph; Sottie Moses; Sottie Stephen; Christian Tette; Kanu Okonipa; Daniel Koyepti; da Kanu Natte.

NDLEA
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
NDLEA Ta Cafke Mai Juna Biyu, Uwa Mai Shayarwa Da Dalibar Jami’a Kan Safaran Miyagun Kwayoyi

NDLEA Ta Cafke Mai Juna Biyu Da Dalibin Jami'a Kan Safarar Miyagun Kwayoyi

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.