ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Cafke Mai Juna Biyu, Uwa Mai Shayarwa Da Dalibar Jami’a Kan Safaran Miyagun Kwayoyi

by Khalid Idris Doya
4 years ago
NDLEA

Hukumar dakile safaran miyagun kwayoyi (NDLEA) ta cafke wata mata mai juna biyu da wata uwa mai jego da wata dalibar jami’a ‘yar aji biyu kan safaran miyagun kwayoyi.

Hukumar ta NDLEA ta ce, wadanda ake zargin su na daga cikin mutum 28 ne da ta kama da tabar Wiwi mai nauyin kilogiram 9,437.7 da tabulet din maganin opioids da sauran miyagun kwayoyi a samamen da ta gudanar a jihohin 12 da suka kunshi: Yobe, Ondo, Edo, Rivers, Akwa Ibom, Imo, Jigawa, Kogi, Adamawa, Kaduna, Kwara, Lagos da kuma babban birnin tarayya Abuja.

  • NDLEA Ta Cafke Ƙwayar Tramadol Miliyan 13 Boye Cikin Wani Gida A Legas

Kakakin hukumar ta NDLEA, Femi Babafemi a FCT, ya ce, dakarunsu a ranar Asabar 15 ga watan Oktoba sun mamayi wani kauye mai suna Chukuku, mai nisan kilomita 10 da Gwagwalada inda suka gano wani katafaren rumbun boye tabar Wiwi.

ADVERTISEMENT

Inda aka kamo jumbo 510 na haramtattun tabar masu nauyin kilogiram 5, 640 tare da cafke wata mata mai shayarwa Sa’adatu Abdullahi, ‘yar shekara 35, da take kula da rumbun.

A jihar Yobe kuwa hukumar ta kama kilograms na tabar Wiwi 48 a Buni Yadi, kuma sun mamayi wani wuri da ke Potiskum inda suka kamo kilograms na tabar 31 daga wajen mutum biyu da ake zargi Mohammed Mamuda da wata matar aure mai juna biyu, Hauwa Haruna.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Kazalika, wata dalibin jami’ar karatu daga gida (NOUN) da ke karanta ilimin aikin jarida, Ms. Mercy Nyong, ‘yar shekara 30 a duniya, a ranar Laraba 12 ga watan Oktaba.ne ta fada tarkon hukumar a filin sauka da tashi na Jirgin saman kasa da kasa ta Murtala Muhammad da ke Ikeja, Legas a kokarinta na fita da garam 300 na Tramadol samfurin 225mg cikin abun boye turare zuwa Dubai.

Sannan wasu ‘yan kasar Ghana su 9 an cafke su a kokarinsu na yin safaran kilograms 10,843.95 na tabar Wiwi ta tekun Nijeriya, inda kuma a ranar Juma’a 14 ga watan Oktoba aka yanke musu hukuncin zaman gidan yari na shekara 72.

Da fari dai jami’an hukumar tsaron farin kaya ta NSCDC ne suka kama su kana suka mikasu ga hukumar NDLEA domin fadada bincike da gurfanar da su.

A karshe dai an gurfanar da su a kotu kan kara mai lamba FHC/L/292C/2021.

Da yake yanke hukunci a ranar Juma’a, Mai Shari’a Akintayo Aluko na babban kotun tarayya da ke Legas ya kama tare da daure ‘yan Ghana din bisa safaran Wiwi inda ya daure kowannesu shekara takwas a gidan yari.

Wadanda aka dauren su ne: Victor Wuddah; Freeman Gazul; Adotete Joseph; Sottie Moses; Sottie Stephen; Christian Tette; Kanu Okonipa; Daniel Koyepti; da Kanu Natte.

NDLEA
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
NDLEA Ta Cafke Mai Juna Biyu, Uwa Mai Shayarwa Da Dalibar Jami’a Kan Safaran Miyagun Kwayoyi

NDLEA Ta Cafke Mai Juna Biyu Da Dalibin Jami'a Kan Safarar Miyagun Kwayoyi

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.