ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Da Kasar China, Sun Sake Sabunta Yarjejeniyar Musayar Takardun Kudade Ta Naira Tiriliyan 3.28

by Abubakar Abba
1 year ago
Nijeriya

Shekaru shida bayan yarjejeniyar musayar takardun kudade ta kasa da kasa, da aka kulllan Babban Bankin Kasar China da Bakin Alumma na kasar China, sun sake sabunta yarjejeniyar da Babban Bankin Nijeriya CBN.

Gundarin kudin yarjejeniyar, ta kai Naira tiriliyan 3.28 ko kuma Naira biliyan 15, na kudin kasar China wato yuan, wacce ta kai kwatankwacin dala biliyan 2.09.

  • Gwamnan Kano Ya Yi Sabbin Naɗe-Naɗe
  • Dokar Haraji Za Ta Ƙara Jefa Al’umma Cikin Talauci – Gwamnatin Kano

A cikin wata sanarwa da Babban Bankin na kasar China ya wallafa a shafinsa na Internet, wa’adin yarjejeniyar za ta kai ta shekaru uku, wacce kuma za a iya sake sabunta yarjejeniyar idan bukatar hakan taso.

ADVERTISEMENT

Sanarwa ta kara da cewa, sake sabunta wannan yarjejiniyar za ta kara karfafa hada-hadar hadaka a tsakanin China da Nijeriya, tare da kuma kara fadada yin amfani da takardun kudaden kasashen biyu da kara bunkasa hada-hadar kawunaci da kuma zuba hannun jari.

Kazalika, sabunta yarjejeniyar za ta taimakawa kasashen biyu, wajen rage dogaro a kan takardar dalar Amurka don gudanar da hada-hadar kasuwanci.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Tun farko dai, an kulla wannan yarjejeniyar ce, a watan Afirilun 2018 wacca kuma take da wa’adi na shekara uku, duba da yadda ake fuskantar karancin dalar Amurka a kasar nan.

Bugu da kari, jarjejeniyar za ta kara fadada yin amfani da tardun kudi na kasashen biyu tare da kuma kara karfafa hada-hadar kudade,

Nijeriya dai, ta kasance babba wajen yin hadaka, domin kasar ta China, na shigo da danyen mai, iskar Gas wanda daga baya, inda su kuma suke shigo da sauran kaya da bana da ba, ciki har da ababen hawa da na’urorin kayan wutar lantarki daga kasar ta China.

A 2023, Nijeriya ta shigo da kayan daga kasar China, da kudinsu ya kai na dala biliyan 11.2, inda kuma kayan da aka fitar daga kasar zuwa Asiya, kudinsu ya kai dala biliyan 2.4.

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima, ya bayyana cewa, a 2023 yawan hada-hadar kasuwancin d aka yi a tsakanin Nieroya da kasar China, ta kai ta yawan dala biliyan 22.6.

Kashim

Kashim ya bayyana haka ne, a cikin watan Numbar 2024, a fadar shugaban kasa da ke Abuja, a yayin da ya karbi bakuncin wata tawaga daga kasar China.

Mataimakin kwamitin dindin na kungiyar kasar China NPC  Mista Zhang Kingwei ne, ya jagoranci tawagar a lokacin ziyarar.

Shettima ya kara da cewa, huddar jakadanci da ke a tsakanin Nijeriya da China, na kara fadada a duk shekara zuwa kashi 33.

Tabbasa Nijeriya ta kasance, babbar kawar kasar China wajen yin hadaka, musamman wajen zuba hannun jari a fannonin bunkasa tatttalin arzkin Nijeriya.

Misali, dangantar kasuwanci a tsakanin kasashen biyu ta kwanan baya, an mayar da hankali ne, wajen aikin samar da makamashi ga Nijeriya.

Nijeriya
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Next Post
CMG Ta Gudanar Da Rahaza Karo Na 1 Na Shagalin Murnar Sabuwar Shekarar 2025 Bisa Kalandar Gargajiyar Kasar Sin

CMG Ta Gudanar Da Rahaza Karo Na 1 Na Shagalin Murnar Sabuwar Shekarar 2025 Bisa Kalandar Gargajiyar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.