ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Da Saudiyya Sun Ƙara Ƙarfafa Alaƙa Kan Inganta Harkokin Hajji Da Umrah

by Leadership Hausa
7 months ago
NAHCON

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya da Masarautar Saudiyya sun sake jaddada aniyarsu ta ƙarfafa haɗin guiwa a harkokin gudanar da Hajji da Umrah, biyo bayan wani muhimmin taro da manyan jami’an ƙasashen biyu suka gudanar an Abuja.

Mai taimakawa Shugaban NAHCON a bangaren yada labarai, Ahmad Mu’azu, ya ce taron ya haɗa hukumomin Nijeriya da wata tawaga daga Saudiyya ƙarƙashin jagorancin Ministan Hajji da Umrah na Masarautar Saudiyya, Dakta Tawfiq Al-Rabiah. An bayyana ziyarar a matsayin wata muhimmiyar alama ta ƙara ƙarfafa dangantaka tsakanin ƙasashen biyu, musamman wajen kula da alhazan Nijeriya.

  • Gwamnatin Kano Ta Amince Da Ɗaukar Likitoci ‘Yan Asalin Jihar Aiki Kai-tsaye
  • Kotu Ta Yanke Wa Ɗan Fashi Hukuncin Kisa A Nasarawa

Da yake maraba da tawagar, Shugaban Hukumar Kula da Hajji ta Ƙasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Usman, ya ce ziyarar ta nuna ci gaba da haɗin guiwar Saudiyya da Nijeriya wajen yi wa Baƙin Allah hidima. Ya yaba wa Masarautar bisa ƙoƙarinta na inganta jin daɗin alhazai da samar da ababen more rayuwa da tabbatar da tsaro da kuma inganta ayyukan Hajji da Umrah, musamman ta hanyar shirin Saudi ‘Vision 2030’.

ADVERTISEMENT

Farfesa Abdullahi Usman ya gamsu cewa akwai wasu ƙalubale da suka shafi bizar Umrah ga ’yan Nijeriya, musamman matsalar tsawaita zama bayan wa’adin izini daga wasu alhazai. Ya jaddada cewa Nijeriya za ta yi aiki kafada da kafada da hukumomin Saudiyya domin shawo kan matsalar, ta hanyar tsaurara sa ido kan kamfanonin da ke da lasisi da inganta tsarin bayanai da kuma wayar da kan allumma.

Ya kuma tabbatar da cewa NAHCON za ta bi duk ƙa’idoji da umarnin Ma’aikatar Hajji da Umrah ta Saudiyya, tare da kare mutuncin harkokin Hajji da Umrah da muradun alhazan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

A jawabinsa, Ministan Harkokin Wajen Nijeriya, Yusuf Maitama Tuggar, ya bayyana ziyarar a matsayin tarihi, yana mai cewa wannan ne karo na farko da Ministan Hajji da Umrah na Saudiyya ya ziyarci Nijeriya. Ya isar da gaisuwa da fatan alheri daga Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ga Sarki Salman bin Abdulaziz Al-Saud da kuma Yarima mai jiran gado, Muhammad bin Salman.

Ministan ya ce Shugaba Tinubu yana matuƙar girmama Saudiyya, tare da ƙudirin ƙarfafa tsohuwar dangantaka mai ɗorewa tsakanin ƙasashen biyu. Ya ƙara da cewa haɗin guiwa a harkokin Hajji da Umrah na daga cikin muhimman ginshiƙan alaƙar Nijeriya da Saudiyya, wadda ta samo asali daga addini da dadaddiyar alaƙar al’umman biyu.

A nasa ɓangaren, Ministan Hajji da Umrah na Saudiyya, Dakta Tawfiq Al-Rabiah, ya bayyana cewa Masarautar na da cikakken shiri na ci gaba da aiki tare da Nijeriya domin tabbatar da sauƙi da tsaro ga alhazan Nijeriya. Ya ce a shekarar 2025, sama da ’yan Nijeriya 89,000 ne suka gudanar da Umrah, inda kashi 92 cikin 100 suka shiga Saudiyya da bizar Umrah.

Ya ƙara da cewa an samar da kusan jirage 420 daga Jeddah domin tallafa wa harkokin Umrah ga ’yan Nijeriya, yana mai nuna fatan ci gaba da haɗin guiwa wajen shirin Hajjin 1447 Hijira (2026), domin inganta tsaro da ayyuka da sauƙaƙe harkokin Hajji da Umrah.

A ƙashen taron, ɓangarorin biyu sun amince da ci gaba da haɗin kai da ɗaukar matakai masu amfani domin inganta harkokin Hajji da Umrah, tare da tabbatar da jin daɗi da kare mutuncin alhazan Nijeriya, Baƙin Allah da al’ummar Musulmi baki ɗaya.

NAHCON
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
’Yan Bindiga Sun Kashe Mutane, Sun Ƙone Gidaje A Ƙauyukan Kwara

’Yan Bindiga Sun Kashe Mutane, Sun Ƙone Gidaje A Ƙauyukan Kwara

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.