ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Da Saudiyya Sun Ƙara Ƙarfafa Alaƙa Kan Inganta Harkokin Hajji Da Umrah

by Leadership Hausa
5 months ago
NAHCON

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya da Masarautar Saudiyya sun sake jaddada aniyarsu ta ƙarfafa haɗin guiwa a harkokin gudanar da Hajji da Umrah, biyo bayan wani muhimmin taro da manyan jami’an ƙasashen biyu suka gudanar an Abuja.

Mai taimakawa Shugaban NAHCON a bangaren yada labarai, Ahmad Mu’azu, ya ce taron ya haɗa hukumomin Nijeriya da wata tawaga daga Saudiyya ƙarƙashin jagorancin Ministan Hajji da Umrah na Masarautar Saudiyya, Dakta Tawfiq Al-Rabiah. An bayyana ziyarar a matsayin wata muhimmiyar alama ta ƙara ƙarfafa dangantaka tsakanin ƙasashen biyu, musamman wajen kula da alhazan Nijeriya.

  • Gwamnatin Kano Ta Amince Da Ɗaukar Likitoci ‘Yan Asalin Jihar Aiki Kai-tsaye
  • Kotu Ta Yanke Wa Ɗan Fashi Hukuncin Kisa A Nasarawa

Da yake maraba da tawagar, Shugaban Hukumar Kula da Hajji ta Ƙasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Usman, ya ce ziyarar ta nuna ci gaba da haɗin guiwar Saudiyya da Nijeriya wajen yi wa Baƙin Allah hidima. Ya yaba wa Masarautar bisa ƙoƙarinta na inganta jin daɗin alhazai da samar da ababen more rayuwa da tabbatar da tsaro da kuma inganta ayyukan Hajji da Umrah, musamman ta hanyar shirin Saudi ‘Vision 2030’.

ADVERTISEMENT

Farfesa Abdullahi Usman ya gamsu cewa akwai wasu ƙalubale da suka shafi bizar Umrah ga ’yan Nijeriya, musamman matsalar tsawaita zama bayan wa’adin izini daga wasu alhazai. Ya jaddada cewa Nijeriya za ta yi aiki kafada da kafada da hukumomin Saudiyya domin shawo kan matsalar, ta hanyar tsaurara sa ido kan kamfanonin da ke da lasisi da inganta tsarin bayanai da kuma wayar da kan allumma.

Ya kuma tabbatar da cewa NAHCON za ta bi duk ƙa’idoji da umarnin Ma’aikatar Hajji da Umrah ta Saudiyya, tare da kare mutuncin harkokin Hajji da Umrah da muradun alhazan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

A jawabinsa, Ministan Harkokin Wajen Nijeriya, Yusuf Maitama Tuggar, ya bayyana ziyarar a matsayin tarihi, yana mai cewa wannan ne karo na farko da Ministan Hajji da Umrah na Saudiyya ya ziyarci Nijeriya. Ya isar da gaisuwa da fatan alheri daga Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ga Sarki Salman bin Abdulaziz Al-Saud da kuma Yarima mai jiran gado, Muhammad bin Salman.

Ministan ya ce Shugaba Tinubu yana matuƙar girmama Saudiyya, tare da ƙudirin ƙarfafa tsohuwar dangantaka mai ɗorewa tsakanin ƙasashen biyu. Ya ƙara da cewa haɗin guiwa a harkokin Hajji da Umrah na daga cikin muhimman ginshiƙan alaƙar Nijeriya da Saudiyya, wadda ta samo asali daga addini da dadaddiyar alaƙar al’umman biyu.

A nasa ɓangaren, Ministan Hajji da Umrah na Saudiyya, Dakta Tawfiq Al-Rabiah, ya bayyana cewa Masarautar na da cikakken shiri na ci gaba da aiki tare da Nijeriya domin tabbatar da sauƙi da tsaro ga alhazan Nijeriya. Ya ce a shekarar 2025, sama da ’yan Nijeriya 89,000 ne suka gudanar da Umrah, inda kashi 92 cikin 100 suka shiga Saudiyya da bizar Umrah.

Ya ƙara da cewa an samar da kusan jirage 420 daga Jeddah domin tallafa wa harkokin Umrah ga ’yan Nijeriya, yana mai nuna fatan ci gaba da haɗin guiwa wajen shirin Hajjin 1447 Hijira (2026), domin inganta tsaro da ayyuka da sauƙaƙe harkokin Hajji da Umrah.

A ƙashen taron, ɓangarorin biyu sun amince da ci gaba da haɗin kai da ɗaukar matakai masu amfani domin inganta harkokin Hajji da Umrah, tare da tabbatar da jin daɗi da kare mutuncin alhazan Nijeriya, Baƙin Allah da al’ummar Musulmi baki ɗaya.

NAHCON
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
’Yan Bindiga Sun Kashe Mutane, Sun Ƙone Gidaje A Ƙauyukan Kwara

’Yan Bindiga Sun Kashe Mutane, Sun Ƙone Gidaje A Ƙauyukan Kwara

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.