Kamfanin taliyar Indomie ya sake gudanar da taron rabon kyaututtuka a jihohin Kano, Kaduna da Sakkwato a matsayin wani ɓangare na ci gaba da gasar “Garabasar Samun Nasara”, inda aka bayyana tare da karrama sabbin masu nasara na wannan wata.
Shirin, wanda ya haɗa bayar da kyaututtuka da kuma nishaɗantar da jama’a, na ci gaba da jan hankalin kwastomomi daga sassa daban-daban na Arewacin Nijeriya.
An gudanar da taron ne a Bata da ke Kasuwar Singer a Kano, Tsohuwar Kasuwa a Sakkwato, da kuma Babbar Kasuwa a Kaduna, a ranar Litinin, 20 ga Afrilu, 2026. Taron ya samu halartar ’yan kasuwa, masu sayayya da kuma kwastomomin Indomie, inda suka shaida rabon kyaututtuka kai tsaye ga masu nasara.
Hanyoyin Shiga Gasar
Masu shiga gasar suna shiga ne ta hanyar miƙa ledojin sabon fakitin Indomie a cibiyoyin karɓa da aka tanada.
Domin shiga, ana buƙatar:
• Miƙa sabon faketin ledojin Indomie guda 10 domin samun fakitin Indomie gram 70 kyauta nan take
• Duk leda 10 da aka kai suna a matsayin zama maki ɗaya, wanda ke ƙara bayar da damar shiga jerin masu nasara na wata-wata
A yayin taron, an gudanar da wasanni da dama domin nishaɗantar da mahalarta tare da ƙarfafa dangantaka tsakanin kamfanin da kwastomominsa.
Yayin da gasar ke ƙara armashi, mahalarta na fafatawa domin shiga cikin mutane 80 na farko, waɗanda ake karramawa da kyaututtuka a ƙarshen kowane wata.
Rabon Kyaututtuka
Masu nasara suna samun kyaututtuka daban-daban da suka haɗa da:
• Na’urar wasan PS5
• Wayoyin iPhone
• Firiza
• Murhun gas
• Talabijin
• Fanka
• Kekuna
Ra’ayoyin Masu Nasara
Ɗaya daga cikin wadanda suka ci nasara ya bayyana farin cikinsa yana mai cewa:
“Na ji daɗi ƙwarai da wannan shiri. Gaskiya ne kuma yana da amfani. Ina ƙarfafa wa kowa gwiwa ya shiga.”
Baya ga kyaututtuka da nishaɗi, gasar ta taimaka wajen bunƙasa harkokin kasuwanci a kasuwanni, inda aka samu ƙarin jama’a da haɓakar ciniki a wuraren da aka gudanar da taron.
A yayin bikin rabon kyautukan Wakilan kamfanin Indomie sun bayyana cewa: “Mun ƙirƙiro wannan gasar ne domin nuna godiya ga kwastomominmu tare da ƙara kusantar al’umma.”
Ana iya bibiyar jadawalin mutanen da suka yi nasara kai tsaye ta shafin Indomie.ng/arewa, tare da samun sabbin bayanai ta shafukan sada zumunta na Indomie Arewa.
Kamfanin Indomie yana ƙarfafa wa jama’a guiwa da su ci gaba da shiga gasar, domin samun damar shiga jerin masu nasara na watanni masu zuwa yayin da rabon kyaututtuka ke ci gaba da gudana a faɗin jihohin Arewacin Nijeriya.
Kamfanin taliyar Indomie ya sake gudanar da taron rabon kyaututtuka a jihohin Kano, Kaduna da Sakkwato a matsayin wani ɓangare na ci gaba da gasar “Garabasar Samun Nasara”, inda aka bayyana tare da karrama sabbin masu nasara na wannan wata.
Shirin, wanda ya haɗa bayar da kyaututtuka da kuma nishaɗantar da jama’a, na ci gaba da jan hankalin kwastomomi daga sassa daban-daban na Arewacin Nijeriya.
An gudanar da taron ne a Bata da ke Kasuwar Singer a Kano, Tsohuwar Kasuwa a Sakkwato, da kuma Babbar Kasuwa a Kaduna, a ranar Litinin, 20 ga Afrilu, 2026. Taron ya samu halartar ’yan kasuwa, masu sayayya da kuma kwastomomin Indomie, inda suka shaida rabon kyaututtuka kai tsaye ga masu nasara.
Hanyoyin Shiga Gasar
Masu shiga gasar suna shiga ne ta hanyar miƙa ledojin sabon fakitin Indomie a cibiyoyin karɓa da aka tanada.
Domin shiga, ana buƙatar:
• Miƙa sabon faketin ledojin Indomie guda 10 domin samun fakitin Indomie gram 70 kyauta nan take
• Duk leda 10 da aka kai suna a matsayin zama maki ɗaya, wanda ke ƙara bayar da damar shiga jerin masu nasara na wata-wata
A yayin taron, an gudanar da wasanni da dama domin nishaɗantar da mahalarta tare da ƙarfafa dangantaka tsakanin kamfanin da kwastomominsa.
Yayin da gasar ke ƙara armashi, mahalarta na fafatawa domin shiga cikin mutane 80 na farko, waɗanda ake karramawa da kyaututtuka a ƙarshen kowane wata.
Rabon Kyaututtuka
Masu nasara suna samun kyaututtuka daban-daban da suka haɗa da:
• Na’urar wasan PS5
• Wayoyin iPhone
• Firiza
• Murhun gas
• Talabijin
• Fanka
• Kekuna
Ra’ayoyin Masu Nasara
Ɗaya daga cikin wadanda suka ci nasara ya bayyana farin cikinsa yana mai cewa:
“Na ji daɗi ƙwarai da wannan shiri. Gaskiya ne kuma yana da amfani. Ina ƙarfafa wa kowa gwiwa ya shiga.”
Baya ga kyaututtuka da nishaɗi, gasar ta taimaka wajen bunƙasa harkokin kasuwanci a kasuwanni, inda aka samu ƙarin jama’a da haɓakar ciniki a wuraren da aka gudanar da taron.
A yayin bikin rabon kyautukan Wakilan kamfanin Indomie sun bayyana cewa: “Mun ƙirƙiro wannan gasar ne domin nuna godiya ga kwastomominmu tare da ƙara kusantar al’umma.”
Ana iya bibiyar jadawalin mutanen da suka yi nasara kai tsaye ta shafin Indomie.ng/arewa, tare da samun sabbin bayanai ta shafukan sada zumunta na Indomie Arewa.
Kamfanin Indomie yana ƙarfafa wa jama’a guiwa da su ci gaba da shiga gasar, domin samun damar shiga jerin masu nasara na watanni masu zuwa yayin da rabon kyaututtuka ke ci gaba da gudana a faɗin jihohin Arewacin Nijeriya.















Discussion about this post