ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

by Yusuf Shuaibu
3 weeks ago
APC

Bayan kammala zaben fid da gwani don tantance ‘yan takarar shugaban kasa a zaben 2027, jam’iyyun siyasa sun mayar da hankali kan zabar abokan takarar shugaban kasa.

Rahotanni sun nuna cewa wasu jam’iyyun suna fuskantar kalubale wajen yanke hukunci. Duk da cewa suna da lokaci har zuwa ranar 27 ga Yuni don saka cikakkun bayanan ‘yan takarar shugaban kasa da abokan takararsu ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), masu ruwa da tsaki suna jin matsin lamba don kammala zabukansu.

An ruwaito cewa jam’iyyar masu mulki ta APC, na kan gaba wajen fuskantar wadannan matsaloli. Majiyoyi sun nuna cewa batutuwan da ba a warware ba da suka shafi zaben mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima har yanzu ana tattaunawa a kansu. Duk da cewa cikakken bayani game da wadannan batutuwan yana ga Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, ba a kai ga kai karshensu ba, inda sunaye daban-daban ke bayyana a matsayin masu yiwuwar maye gurbinsa. Wani muhimmin bangare na tsarin zaben shi ne, bukatar daidaito na addini. Wannan ya kawo sunaye irin su tsohon shugaban majalisar wakilai, Hon. Yakubu Dogara, da ministan tsaro, Janar Christopher Musa. Duk da haka, masu goyon bayan ci gaba da tikitin Musulmi-Musulmi suna ikirarin cewa tasirin cire Shettima za a iya rage shi ta hanyar zabar wani kamar mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaron kasa, Malam Nuhu Ribadu, wanda ya fito daga Adamawa a arewa maso gabas, yanki daya da Shettima.

ADVERTISEMENT

A halin yanzu, tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, wanda ya kasance dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar ADC, shi ma yana fama da matsalar zaben mataimakin takara. Sunayen da ake duba sun hada da tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi, da tsohon mataimakin shugaban majalisar wakilai, Hon. Emeka Ihedioha.

Sai dai kuma majiyoyi na nuna cewa tattaunawa har yanzu na ci gaba, kuma an yi hasashen cewa Amaechi na iya kin karbar damar zama mataimakin dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar a zaben 2027. Wasu majiyoyi sun tabbatar da cewa tsohon gwamnan Jihar Ribas na jiran tayin a hukumance daga jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

Wata majiya me tushe da ke kusa da ADC ta ce jam’iyyar na kokarin zaben mataimaki dan takarar shugaban ne a hankali kuma tana da niyyar kammala tattaunawa kafin wa’adin INEC. “Ana ci gaba da aiwatar da tsarin jam’iyyar. Muna kokarin yin hakan cikin hikima,” in ji majiyar.

Wata majiya da ta musanta zargin cewa Amaechi zai iya kin karbar tayin, ta bayyana cewa tsohon gwamnan Jihar Ribas na jiran a gabatar da tayin hukumance ne. Majiyar ta kara bayyana cewa tattaunawa na ci gaba a matakin jam’iyya da na ‘yan takara. Suna gudanar da tattaunawa, kuma da zarar sun cimma matsaya, za a sanar.

Haka kuma, wata majiya ta nuna cewa Atiku a baya ya yi la’akari da zabar abokin takara daga yankin kudu maso yamma na kasar nan.  Majiyar ta ce tattaunawar ta ci gaba, inda ake tsammanin cewa Atiku zai zabi abokin takararsa daga kudu maso yamma.

Daga cikin manyan jam’iyyun siyasa guda uku a fafatawar zaben shugaban kasa na 2027, APC da ADC da NDC, jam’iyyar NDC ne kadai ta warware batun abokin takarar shugaban kasa. Dan takararta, Mista Peter Obi, ya sanar cewa tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, zai kasance abokin takararsa. Sauran jam’iyyun, ciki har da APC mai mulki da ADC mai hamayya, har yanzu suna cikin tattaunawa mai zurfi don tantance wadanda za su iya kasancewa mafi inganci a matsayin abokan takararsu.

Bangarori biyu na jam’iyyar PDP, wadanda suka zabi tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan da Sanata Sandy Onor, a matsayin dan takarar shugaban kasa da mataimaki na ci gaba da kasancewa cikin rashin tabas. Haka kuma, dan takarar jam’iyyar AP, Gbenga Olawepo-Hashim, bai sanar da mataimakinsa ba. Ita ma jam’iyyar SDP na fuskantar irin wannan lamari, wadda a halin yanzu ke da ‘yan takarar shugaban kasa na bangarori.

APC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

MASU ALAKA

makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

June 26, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Next Post
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

July 4, 2026
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.