Bayan kammala zaben fid da gwani don tantance ‘yan takarar shugaban kasa a zaben 2027, jam’iyyun siyasa sun mayar da hankali kan zabar abokan takarar shugaban kasa.
Rahotanni sun nuna cewa wasu jam’iyyun suna fuskantar kalubale wajen yanke hukunci. Duk da cewa suna da lokaci har zuwa ranar 27 ga Yuni don saka cikakkun bayanan ‘yan takarar shugaban kasa da abokan takararsu ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), masu ruwa da tsaki suna jin matsin lamba don kammala zabukansu.
An ruwaito cewa jam’iyyar masu mulki ta APC, na kan gaba wajen fuskantar wadannan matsaloli. Majiyoyi sun nuna cewa batutuwan da ba a warware ba da suka shafi zaben mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima har yanzu ana tattaunawa a kansu. Duk da cewa cikakken bayani game da wadannan batutuwan yana ga Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, ba a kai ga kai karshensu ba, inda sunaye daban-daban ke bayyana a matsayin masu yiwuwar maye gurbinsa. Wani muhimmin bangare na tsarin zaben shi ne, bukatar daidaito na addini. Wannan ya kawo sunaye irin su tsohon shugaban majalisar wakilai, Hon. Yakubu Dogara, da ministan tsaro, Janar Christopher Musa. Duk da haka, masu goyon bayan ci gaba da tikitin Musulmi-Musulmi suna ikirarin cewa tasirin cire Shettima za a iya rage shi ta hanyar zabar wani kamar mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaron kasa, Malam Nuhu Ribadu, wanda ya fito daga Adamawa a arewa maso gabas, yanki daya da Shettima.
A halin yanzu, tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, wanda ya kasance dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar ADC, shi ma yana fama da matsalar zaben mataimakin takara. Sunayen da ake duba sun hada da tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi, da tsohon mataimakin shugaban majalisar wakilai, Hon. Emeka Ihedioha.
Sai dai kuma majiyoyi na nuna cewa tattaunawa har yanzu na ci gaba, kuma an yi hasashen cewa Amaechi na iya kin karbar damar zama mataimakin dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar a zaben 2027. Wasu majiyoyi sun tabbatar da cewa tsohon gwamnan Jihar Ribas na jiran tayin a hukumance daga jam’iyyar.
Wata majiya me tushe da ke kusa da ADC ta ce jam’iyyar na kokarin zaben mataimaki dan takarar shugaban ne a hankali kuma tana da niyyar kammala tattaunawa kafin wa’adin INEC. “Ana ci gaba da aiwatar da tsarin jam’iyyar. Muna kokarin yin hakan cikin hikima,” in ji majiyar.
Wata majiya da ta musanta zargin cewa Amaechi zai iya kin karbar tayin, ta bayyana cewa tsohon gwamnan Jihar Ribas na jiran a gabatar da tayin hukumance ne. Majiyar ta kara bayyana cewa tattaunawa na ci gaba a matakin jam’iyya da na ‘yan takara. Suna gudanar da tattaunawa, kuma da zarar sun cimma matsaya, za a sanar.
Haka kuma, wata majiya ta nuna cewa Atiku a baya ya yi la’akari da zabar abokin takara daga yankin kudu maso yamma na kasar nan. Majiyar ta ce tattaunawar ta ci gaba, inda ake tsammanin cewa Atiku zai zabi abokin takararsa daga kudu maso yamma.
Daga cikin manyan jam’iyyun siyasa guda uku a fafatawar zaben shugaban kasa na 2027, APC da ADC da NDC, jam’iyyar NDC ne kadai ta warware batun abokin takarar shugaban kasa. Dan takararta, Mista Peter Obi, ya sanar cewa tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, zai kasance abokin takararsa. Sauran jam’iyyun, ciki har da APC mai mulki da ADC mai hamayya, har yanzu suna cikin tattaunawa mai zurfi don tantance wadanda za su iya kasancewa mafi inganci a matsayin abokan takararsu.
Bangarori biyu na jam’iyyar PDP, wadanda suka zabi tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan da Sanata Sandy Onor, a matsayin dan takarar shugaban kasa da mataimaki na ci gaba da kasancewa cikin rashin tabas. Haka kuma, dan takarar jam’iyyar AP, Gbenga Olawepo-Hashim, bai sanar da mataimakinsa ba. Ita ma jam’iyyar SDP na fuskantar irin wannan lamari, wadda a halin yanzu ke da ‘yan takarar shugaban kasa na bangarori.














Discussion about this post