Wani tsagi na jam’iyyar NNPP ƙarƙashin jagorancin Boniface Aniebonam ya zargi INEC da hana jam’iyyar kammala tantance ‘yan takara da gudanar da zaɓen fidda gwani gabanin zaɓen 2027.
Jam’iyyar ta kuma yi barazanar shirya zanga-zanga a Abuja, tana mai zargin cewa INEC na ci gaba da yin watsi da umarnin kotu da suka shafi rikicin shugabancin jam’iyyar. A cikin wata sanarwa da sakataren jam’iyyar na ƙasa, Ogini Olaposi, ya fitar ranar Alhamis, ya ce jinkirin da hukumar ke yi na iya shafar damar NNPP ta shiga zaɓen 2027.
Olaposi ya ce jam’iyyar ta bi duk hanyoyin doka domin ganin INEC ta bi umarnin kotu, amma har yanzu ba a ɗora sahihin tsarin shugabancin jam’iyyar a shafin hukumar ba. Ya kuma yi zargin cewa wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta umarci INEC ta amince da kwamitin gudanarwa na jam’iyyar ƙarƙashin Agbo Major tare da cire tsarin Rabiu Musa Kwankwaso daga jam’iyyar cikin sa’o’i 72, amma har yanzu ba a aiwatar da hukuncin ba.
Jam’iyyar ta ce tana da haƙƙin gudanar da zanga-zanga cikin lumana idan har INEC ta ci gaba da kin bin hukuncin kotu, tana mai cewa ba za ta amince a hana ta shiga tsarin zaɓe a matsayin halastacciyar jam’iyya mai rijista a Nijeriya ba.















Discussion about this post