ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NSCDC Ta Tura Jami’ai 10,210 Da Za Su Sanya Ido A Zaɓen Gwamnan Jihar Osun

by El-Zaharadeen Umar
4 weeks ago
NSCDC

Shugaban rundunar tsaro ta NSCDC Farfesa Ahmad Abubakar Audi ya bada umarnin a jibge jami’an su mutum 10,210 na musamman domin ƙara ƙarfafa tsaro da kula wajen gudanar da zaɓen jihar Osun

Bayanin haka yana ƙunshe ne a cikin wata sanarwa na jami’in hulɗa da jama’a na rundunar NSCDC na ƙasa Babanwale Afolabi ya fitar a ranar Litinin a Abuja.

Afolabi ya ce jibge jami’an ya fara ne daga ranar Litinin domin tabbatar da cewa masu zaɓe da jami’an zaɓe da masu sanya ido da ƴan jarida da sauran al’umma sun gudanar da zaɓen su ba tare da tashin hankali ko tsoro ba

ADVERTISEMENT

A cewar sanarwar, jami’ai masu sanye da kaki da kuma farin kaya daga jihohin Oyo da Ondo da Ekiti da Ogun da Lagos da Kwara da Edo da Kogi da Delta da tare da birnin tarayya Abuja tuni an jibge su a jihar Osun.

Sanarwar ta cigaba da bayanin cewa a ɗauko jami’ai 1,000 daga kowane runduna 10 domin ƙarfafa tsaro a jihar baki ɗaya kuma za su yi aiki tare da sauran jami’an tsaro a lokacin zaɓen.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Afolabi ya ƙara da cewa jigbe jami’an na daga cikin tsarin inganta tsaro kafin da bayan an kammala zaɓe, ya hanyar bayar tsaro da yanayi mai kyau domin kowa ya gudanar da zaɓe na da cikin kwanciyar hankali.

Haka kuma shugaban rundunar na ƙara ya bada umarnin a ƙara jigbe wasu jami’an na musamman da za su tabbatar da komi yana tafiya yadda aka tsara da suka haɗa da mataimakin shugaba da sashen tattara bayanan sirri da sashen mata ba musanman da kuma sashen ko ta kwana tare da ɓangaren K9

Shugaban rundunar NSCDC ya yi alƙawarin yin aiki bisa doka ta hanyar girmama ƴancin kowa lokacin gudanar da zaɓen tare da tabbatarwa da al’umma an ba su tsaro yadda ya kamata

Sai dai kwamandan ya bayyana cewa ba zai lamunci duk wani jami’in tsaro da za a haɗa kai da shi ba wajen yi wa tsare-tsaren zaɓe karan tsaye ba, musamman ƴan bangar siyasa da ake amfani da su domin lalata tsarin gudanar da zaɓe, duk wanda aka kama zai fuskanci hukunci kamar yadda yake a dokokin zaɓe.

Haka kuma ya yi kira ga ƴan siyasa da magoya baya da al’umma da su tsarawa kan su bin doka domin baiwa dimokuraɗiyya daman wanzuwa.

Ya ƙara da cewa jami’an su za su yi aiki kafaɗa-da kafaɗa da jami’an ƴan sanda ƙarƙashin wani tsari da hukumomin tsaro domin tabbatar da komi ya tafi yadda aka tsara a faɗin ƙananan hukumomi 30 na jihar Osun.

Farfesa Abubakar ya roƙi ruwa da tsaki da suka haɗa da ƴan siyasa da ƴan takara da magoya baya da sauran al’umma da su tattauna bada haɗin kai ga jami’an tsaro da dokokin da hukumar zaɓe ta gindaya.

Sai dai ya ja kunnen al’umma kan duk yunkuri na tada zaune tsaye, wanda ya ce jami’an da na nan cikin shirin ko ta kwana za su aiki a dokance domin tabbatar da doka da oda.

Kazalika ya roƙi al’umma da su zauna lafiya sannan su zama masu lura da sanya ido a lokacin zaɓen, da ƙarfafa jama’a da su riƙa bayar da bayanan ta jami’an tsaro akan duk wani abinda ba su amince da shi ba.

NSCDC
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Cutar Mashako:Yadda Yara Ke Mutuwar Bazata A Jihohin Katsina Da Kano
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mauludin Annabi (SAW): Shugaba Tinubu Ya Nemi A Yi Addu’o’in Nasara Kan Matsalar Tsaro
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Shekaru 8 Cikin Raɗaɗi: Wani Bawan Allah Ya Samu Tiyata Kyauta Daga Gidauniyar Mangal
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Nemi Malamai Su Taimaka Wajen Yaƙi Da Ƴan Ta’adda

MASU ALAKA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Labarai

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Next Post
Jimillar Kudin Shiga Na Fina-Finan Sin Na Shekarar 2026 Ya Wuce Yuan Biliyan 25

Jimillar Kudin Shiga Na Fina-Finan Sin Na Shekarar 2026 Ya Wuce Yuan Biliyan 25

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.