ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Shiga Fargaba Bayan Wike Ya Yi Ganawar Sirri Da Tinubu

by Sadiq
4 years ago
PDP

Wani taron sirri kan makomar siyasar Gwamnan Jihar Ribas Nyesom Wike, ya yi da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu, ya jefa jam’iyyar PDP cikin fargaba.

Wata majiya daga kungiyar yakin neman zaben Tinubu, ta shaida cewa, taron wanda ya samu halartar mutane biyu daga kowanne bangare ya yi albarka.

  • Tilas Ne Gwamnatin Tarayya Ta Dauki Mataki Kan Kisa Sheikh Aisami – Sheikh Bala Lau
  • “Ɗaukar Abdulkarim Daura Matsayin Mataimakin Gwamna Zai Kawo Wa APC Nasara A Katsina”

“Ganawar ta yi mana dadi kuma za a ci gaba da gudanar da makamanciyarta tsakanin bangarorin biyu”, in ji majiyar da ta nemi a sakaya sunanta.

ADVERTISEMENT

Majiyar ta kuma bayyana cewa, wadanda suka halarci taron daga bangaren Tinubu sun hada da Gwamnan Jihar Legas Babajide Sanwo-Olu, da na Jihar Ekiti Kayode Fayemi.

Daga bangaren Wike kuma akwai Gwamnan Jihar Binuwai, Samuel Ortom, da na Jihar Oyo Seyi Makinde.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Rahotanni dai na nuna cewa ana kokarin cimma matsaya ne kan ko Wike zai dawo APC, ko kuma zai yiwa Tinubu aiki daga jam’iyyarsa ta PDP a zaben shugaban kasa na 2023.

Wani tsohon minista da ke tsagin Wike, ya ce bai ga abin tada jijiyar wuya don Wike da Tinubu sun yi taron ba, domin shi ma dan takarar shugaban kasa a PDP Atiku Abubakar na yin makamancinsa da gwamnonin APC.

Yunkurin ji ta bakin Festus Keyamo, kakakin tawagar yakin neman zaben dan takarar APC, da kuma daraktan yada labarai Bayo Onanuga, da kakakin Tinubu, Tunde Rahman, ya ci tura, domin ba su amsa kira da sakonnin da aka tura musu ba.

A hannu guda kuma kakakin Atiku, Paul Ibe ya ki cewa komai kan lamarin.

Tun a baya dai tsohon ministan ayyuka, kuma jigo a jam’iyyar APC, Sanata Adeseye Ogunlewe, ya shawarci Wike da ya koma wajen Tinubu bisa zargin watsi da shi a siyasance da PDP ta yi.

Sai dai a wata hira da tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, ya yi da gidan talabijin na Channels, ya ce babu wanda ya bata wa Wike rai, kuma bai ga abin da aka masa ba.

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Babban Kwamatin Ayyuka Na Jam’iyyar PDP Na kasa Ya Gana Da ‘Yan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar

Babban Kwamatin Ayyuka Na Jam'iyyar PDP Na kasa Ya Gana Da 'Yan Takarar Gwamna Na Jam'iyyar

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.