ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Shiga Fargaba Bayan Wike Ya Yi Ganawar Sirri Da Tinubu

by Sadiq
4 years ago
PDP

Wani taron sirri kan makomar siyasar Gwamnan Jihar Ribas Nyesom Wike, ya yi da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu, ya jefa jam’iyyar PDP cikin fargaba.

Wata majiya daga kungiyar yakin neman zaben Tinubu, ta shaida cewa, taron wanda ya samu halartar mutane biyu daga kowanne bangare ya yi albarka.

  • Tilas Ne Gwamnatin Tarayya Ta Dauki Mataki Kan Kisa Sheikh Aisami – Sheikh Bala Lau
  • “Ɗaukar Abdulkarim Daura Matsayin Mataimakin Gwamna Zai Kawo Wa APC Nasara A Katsina”

“Ganawar ta yi mana dadi kuma za a ci gaba da gudanar da makamanciyarta tsakanin bangarorin biyu”, in ji majiyar da ta nemi a sakaya sunanta.

ADVERTISEMENT

Majiyar ta kuma bayyana cewa, wadanda suka halarci taron daga bangaren Tinubu sun hada da Gwamnan Jihar Legas Babajide Sanwo-Olu, da na Jihar Ekiti Kayode Fayemi.

Daga bangaren Wike kuma akwai Gwamnan Jihar Binuwai, Samuel Ortom, da na Jihar Oyo Seyi Makinde.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Rahotanni dai na nuna cewa ana kokarin cimma matsaya ne kan ko Wike zai dawo APC, ko kuma zai yiwa Tinubu aiki daga jam’iyyarsa ta PDP a zaben shugaban kasa na 2023.

Wani tsohon minista da ke tsagin Wike, ya ce bai ga abin tada jijiyar wuya don Wike da Tinubu sun yi taron ba, domin shi ma dan takarar shugaban kasa a PDP Atiku Abubakar na yin makamancinsa da gwamnonin APC.

Yunkurin ji ta bakin Festus Keyamo, kakakin tawagar yakin neman zaben dan takarar APC, da kuma daraktan yada labarai Bayo Onanuga, da kakakin Tinubu, Tunde Rahman, ya ci tura, domin ba su amsa kira da sakonnin da aka tura musu ba.

A hannu guda kuma kakakin Atiku, Paul Ibe ya ki cewa komai kan lamarin.

Tun a baya dai tsohon ministan ayyuka, kuma jigo a jam’iyyar APC, Sanata Adeseye Ogunlewe, ya shawarci Wike da ya koma wajen Tinubu bisa zargin watsi da shi a siyasance da PDP ta yi.

Sai dai a wata hira da tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, ya yi da gidan talabijin na Channels, ya ce babu wanda ya bata wa Wike rai, kuma bai ga abin da aka masa ba.

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Babban Kwamatin Ayyuka Na Jam’iyyar PDP Na kasa Ya Gana Da ‘Yan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar

Babban Kwamatin Ayyuka Na Jam'iyyar PDP Na kasa Ya Gana Da 'Yan Takarar Gwamna Na Jam'iyyar

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.