Peter Obi ya soki Bola Tinubu kan gaza cika alƙawuran da ya ɗauka na gyara wutar lantarki.
A wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na X, Obi ya ce sama da shekaru biyu bayan Tinubu ya hau mulki, wutar lantarki ba ta inganta yadda ‘yan Nijeriya suka sa rai ba.
- Nahiyar Afrika Ta Yaba Da Sakon Xi Jinping Ga Taron AU
- Larabawan Da Suka Dauki Kasadar Ceton Yahudawa Lokacin Kisan Kiyashi
Ya tuna da maganar da Tinubu ya yi cewa kada mutane su sake zaɓensa idan bai gyara wutar lantarki ba.
Obi ya kuma nuna shakku kan rahotannin cewa gwamnati na shirin komawa amfani da wuta mai amfani da hasken rana aAso Rock, yana mai cewa shugabanni su mayar da hankali wajen inganta wutar lantarki na ƙasa domin talakawa su more yadda ya dace.
Ya ce ‘yan Nijeriya ba sa tsammanin samun cikakkiyar wuta amma suna so a ga yin ƙoƙarin inganta wadda ake da ita.
Obi ya ƙara da cewa shugabanci ya kamata ya kasance tare da talakawa, yana mai jaddada cewa inganta wutar lantarki yana da muhimmanci ga kasuwanci, ci gaban tattalin arziƙi, da rayuwar yau da kullum.















Discussion about this post