Wani matashi mai kimanin shekaru 30 ya rasa ransa a yankin Yenegue da ke Ƙaramar Hukumar Yenagoa, a Jihar Bayelsa.
Rahotanni sun ce wasu mambobin wata ƙungiyar asiri sun kama shi ne bayan ya shiga yankin da ake ganin ba nasu ba ne.
- Majalisar Shari’a Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka A Kan Kwankwaso
- Amurka Ta Ƙwace Kadarorin ‘Yan Nijeriya 8 Da Ake Zargi Da Tallafa Wa Ta’addanci
Sun tsare shi a wani tsohon gini, inda daga baya suka kashe shi.
Majiyoyin tsaro sun ce an gano gawarsa a ɗaure.
Wasu mazauna yankin sun bayyana cewa an daɗe ana rikici tsakanin ƙungiyoyin asiri biyu a wannan waje, kuma wannan na daga cikin abubuwan da ke haddasa tashin hankali.
’Yansanda sun isa wajen domin ɗaukar gawar, kuma sun fara bincike domin gano waɗanda suka aikata laifin.
Kakakin ’yansanda a jihar, DSP Musa Muhammad, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa ana ci gaba da neman waɗanda suka aikata laifin.















Discussion about this post