Dan wasan tsakiyar As Monaco Paul Pogba ya saka hannun jari a kungiyar Al Haboob da ke Saudiyya, wadda ke shirya gasar tseren rakuma a kasar, dan wasan ya zama mai hannun jari kuma jakada ga Al Haboob, kungiyar tseren rakuma ta farko a duniya da ke fafatawa a fadin Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa da Tekun Gulf.
Pogba, mai shekaru 32, ya shaida wa BBC Sport cewa, “Na dauki tsawon lokaci ina saka ido akan wasan tseren rakuma a YouTube kuma na bata lokaci ina yin bincike a lokacin hutuna ina kokarin fahimtar dabarun da ake amfani dasu a wasan, “kuma abin da ya burge ni shi ne irin sadaukarwa da ake yi a wasan wanda ke na bukatar karfin zuciya, sadaukarwa da kuma hadin gwiwa.”
- Li Qiang Ya Gana Da Shugabannin Bankin Duniya Da IMF Da MDD
- Gwamnan Sakkwato Ya Jinjina Wa Sojoji Kan Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Sabon Birni
Gasar tseren rakumi wasa ne na gargajiya wanda ya shahara musamman a Gabas ta Tsakiya, kwallon kafa, tseren rakumi, dambe duka sun fito daga tushe iri daya ne, suna bukatar sadaukarwa mai da hankali, ladabi da jajircewa, wannan shine ke sa a samu nasara a karshe inji dan wasan na kasar Faransa, kungiyar Al Haboob, wadda yan kasuwa Omar Almaeena da Safwan Modir suka kafa, ita ce kungiyar tseren rakuma ta zamani ta farko a duniya da ta fafata a kasashen Duniya
Pogba, wanda ya taba zama dan wasa mafi tsada a Duniya lokacin da ya koma Manchester United daga Juventus a shekarar 2016 akan kudi Yuro miliyan 89, ya kara da cewa “Kasancewata dan wasan kwallon kafa mafi tsada a Duniya abin girmamawa ne, amma kuma sai da nayi aiki tukuru na kuma jure matsin lamba”.













