Babban Darakta Janar na Cibiyar Nazarin Zaman Lafiya da Warware Rikice-rikice (IPCR), Joseph Ochogwu, ya danganta karuwa da rashin tsaro a Nijeriya da raunin tattalin arziki da kuma yawaitar rashin aikin yi a tsakanin matasa, yana mai cewa matasa marasa aikin yi na shiga fashi da makami da sauran laifuka.
Ochogwu ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin wata ziyara da ya kai hedikwatar Media Trust Group a Abuja.
Ya ce raguwar karfin samar da kayayyaki a kasar ya bar matasa da dama ba tare da abin yi ba, lamarin da ke haifar da yanayi mai saukaka aikata laifuka.
“Karfinmu na samar da kayayyaki ya yi rauni. Idan ka zagaya sassa daban-daban na kasar nan, za ka ga matasa ba su da abin yi. A da, suna gona suna noma. Yanzu da yawa daga cikinsu ba sa yi. Wannan karfi da suke da shi yanzu ana karkatar da shi zuwa aikata laifi,” in ji shi.
“Sun sauya daga samar da kayayyaki zuwa aikata laifuka, hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba, fashi da makami da sauran laifuka,” ya kara da cewa.
Ochogwu ya ce gazawar tattalin arziki na daga cikin manyan abubuwan da ke haifar da rikice-rikice a kasar, yana mai jaddada cewa ba za a samu zaman lafiya ba sai an karfafa bangaren samar da kayayyaki.
Ya kuma lura cewa matsalolin tsaro a Nijeriya ba za a iya magance su da karfin soji kadai ba, yana mai kira da a mai da hankali kan hanyoyin warware matsaloli ba tare da amfani da karfi ba.
Babban daraktan IPCR ya yi gargadin cewa lamarin na iya kara tsananta idan ba a dauki matakan gaggawa ba na shigar da matasa cikin ayyukan da za su amfanar da su.















Discussion about this post