Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir Lawal, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar ADC, inda ya zargi shugabannin jam’iyyar da tafka maguɗi a zaben fidda gwani domin fifita ɗan takarar shugaban ƙasa, Atiku Abubakar.
A cikin wata sanarwa da ya fitar, Babachir ya bayyana zaben fidda gwanin a matsayin “abin kunya”, yana mai zargin cewa an sauya sakamako a wurare da dama domin bai wa Atiku da magoya bayansa nasara. Ya ce wasu da suka lashe zabe an maye gurbinsu da mutanen da ke da alaƙa da Atiku.
Babachir ya ce ba zai ci gaba da kasancewa cikin jam’iyyar da, a cewarsa, ke amfani da maguɗi wajen cimma manufofin siyasa ba. Ya ƙara da cewa ba ya son zama wani ɓangare na abin da ya kira “na’urar maguɗin zabe” gabanin babban zaɓen 2027.
Matakin nasa na zuwa ne bayan taƙaddama da ƙorafe-ƙorafen da suka biyo bayan zaɓen fidda gwani na ADC, wanda ya bai wa Atiku tikitin takarar shugaban ƙasa. Ya zuwa yanzu, babu wata sanarwa daga ADC ko Atiku kan zarge-zargen da Babachir ya yi.















Discussion about this post