Tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, na shirin ficewa daga jam’iyyar ADC zuwa Nigeria Democratic Congress (NDC) tare da dubban magoya bayansa. Majiyoyi daga cikin tafiyar Kwankwasiyya sun ce ana sa ran sauya sheƙar zai gudana a mako mai zuwa.
Rahotanni sun nuna cewa matakin ya biyo bayan amincewar shugabannin tafiyar bayan wani muhimmin taro da aka gudanar a gidan Kwankwaso da ke Miller Road a Kano. An kuma bayyana cewa tattaunawa tsakanin bangaren Kwankwaso da NDC ta kai matakin ƙarshe, inda ake jiran kammala wasu ƙananan bayanai kafin sanarwara a hukumance.
Haka kuma, majiyoyi sun ce ana sa ran ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a 2023, Peter Obi, zai shiga sabuwar jam’iyyar tare da Kwankwaso. Manyan jiga-jigan Kwankwasiyya sun kare matakin, suna mai danganta shi da rikice-rikicen da ke addabar ADC.
Ɗaya daga cikin jagororin tafiyar, Dakta Yusuf Kofarmata, ya ce jam’iyyar ADC na fuskantar matsaloli na shari’a da tsarin shugabanci da ka iya kawo cikas ga makomarta. Ya yi nuni da ƙarar kotu da rikicin shugabanci da suka haɗa da soke tarukan jam’iyya da kuma shari’o’i da ke gudana a Kano.
Shi ma wani jagora a tafiyar, Shehu Wada Sagagi, ya ce sun yanke shawarar komawa NDC ne bayan nazari mai zurfi kan barazanar da ke gaban ADC. Ya ƙara da cewa wasu daga cikin magoya baya sun fara ficewa daga jam’iyyar a matakin ƙasa da ƙasa, inda wani jigo a ƙaramar hukumar Dala, Kabiru Adamu Abdullahi, ya sanar da murabus ɗinsa daga ADC bisa umarnin jagororin tafiyar.















Discussion about this post