Kotun koli ta sanya ranar 17 ga Afrilun 2027, domin ci gaba da sauraren shari’ar masarautar Kano.
Kwamitin alkalai, karkashin jagorancin mai shari’a Adamu Jauro, ya dage ci gaba da shari’ar, sakamakon jinkirin da aka samu daga bangaran mai kara a ranakun 14 da 15 ga watan Afrilu, maimakon ya sanar tun kafin lokacin.
Wannan kara dai, ta biyo bayan umarnin da kotun daukaka kara da ke Abuja ta bayar na a mika lamarin ga babbar kotun Jihar Kano, saboda rashin ikon da babbar kotun tarayya ke da shi na sauraren lamarin.
Sai dai, hukuncin da aka yanke a kan sabbin kararrakin da ka shigar masu lambobin CA/KN/27M/2025 da CA/KN/28M/2025, kotun daukaka kara ta amince da cewa; bukatar dakatar da aiwatar da hukuncin da aka yanke a baya da ke jiran daukaka kara a gaban kotun koli ya cancanta.
Kotun daukaka kara ta yanke hukuncin cewa, tun da ya kasance rikicin na sarauta ne, kamata ya yi wata babbar kotun jiha ta yanke hukunci, maimakon babbar kotun tarayya, wadda ta bayyana yin hakan a matsayin wani babban kuskure.
Wata babbar kotun tarayya da ke Kano, a karkashin mai shari’a Abubakar Liman, a ranar 20 ga watan Yunin 2024, ta soke dokar masarautar Kano ta 2024, wadda ta mayar da Muhammadu Sanusi II a matsayin sarki na 16.
Hukuncin farko da babbar kotun tarayya ta yanke, na kallon karar da wani mai ruwa da tsaki a kan lamarin, Aminu Baba-Dan’Agundi ya gabatar, a matsayin wani muhimmin lamari na tabbatar da hakkin bil’adama, sannan kuma ya umarci bangarorin da suka hada da majalisar dokokin Jihar Kano, da su ci gaba da kasancewa da irin wannan matsayi irin na zamanin Sarki Ado Bayero.
Sai dai, kotun daukaka kara a hukuncin da ta yanke, ta bayar da misali da sashe na 251 na kundin tsarin mulkin Nijeriya da kuma sashe na 22(2) na dokar babban kotun tarayya, inda ta ce; batun na sarauta ne da rikicin ‘yan majalisar jiha, don haka ba batun hakki ba ne, ya kamata a gurfanar da shi gaban babbar kotun Jihar Kano ko kuma babbar kotun tarayya da ke babban birnin tarayya Abuja.















Discussion about this post