ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Shugabanci Ya Dabaibaye Ƙungiyoyin Yaƙin Neman Zaɓen Obi Da Kwankwaso

by Yusuf Shuaibu
1 month ago
kwankwaso

Sabon rikicin shugabanci ya dabaibaye ƙungiyar ‘OK Moɓement’, wani dandali na siyasa da aka kafa don tattara goyon baya ga takarar haɗin gwiwar ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, da tsohon gwamnan Kano, Rabiu Kwankwaso, bayan wani taƙƙamar shugabanci mai tsanani da ya haifar da zargin juna, mayar da martanin zargi da kuma iƙirarin shugabanci daban-daban ga ƙungiyar.

Rikicin ya ƙaru ne bayan da ƙungiyar ta sanar da naɗin tsohon shugaban kwamitin shawara kan haɗakar jam’iyyun siyasa, Peter Ameh, a matsayin darakta janar na ƙasa a wata sanarwa da Jackie Wayas ta sanya hannu a kai.

Wayas, wadda ta bayyana kanta a matsayin babban mai jagorantar wannan ƙungiya, ta ce an ɗauki wannan mataki ne biyo bayan taron kwamitin gudanarwa na ƙungiyar.

ADVERTISEMENT

Tsohowar mataimakiyar sakataren yaɗa labarai na jam’iyyar ADC ta ƙara da cewa amincewar da aka yi da naɗin Ameh ta zo ne a haɗin kai saboda ƙwarewarsa a siyasa da jajircewarsa ga ƙa’idodin wannan ƙungiya.

Sai dai, cikin ƴan sa’o’i bayan sanarwar, kalaman sun haddasa cece-kuce bayan wasu mambobin sun tambayi ikon Wayas na kiran kanta a matsayin jagorar a wannan ƙungiya.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

Yunƙurin jin bayani daga Wayas kan lokaci da yadda ta karɓi muƙamin bai samu nasara ba, saboda kiran waya da saƙonnin da aka aika mata ba ta amsa ba har zuwa kammala wannan rahoto.

Sabon rikicin ta bayyana batun rashin jituwa na shugabanci a cikin ƙungiyar.

Yayin da yake magana da manema labarai, tsohon sakatare yaɗa labarai na wannan ƙungiya, Justin Ijeh, ya amince cewa akwai rashin jituwa amma ya dage cewa ya kamata a warware su a cikin gida maimakon ta hanyar kafofin watsa labarai.

A yayin da yake mayar da martani ga iƙirarin cewa akwai rikici tsakanin ƙungiyoyin yaƙin nema Obi da Kwankwaso, Tanko ya dage cewa babu wani rikici a tsakani.

Lokacin da aka tambaye shi ya ƙara fayyace rashin jituwar da ke tsakanin ƙungiyoyin ‘Obidients da na OK, Tanko ya yi watsi da lamarin, yana jaddada cewa babu wata rikici ko rashin jituwa a cikin ƙungiyoyin.

“Da gaske babu wani rikici tsakanimmu. Muna ƙoƙarin yin aiki tare. Muna ƙoƙarin tabbatar da cewa muna aiki tare a matsayin ƙungiya ne kawai,” in ji shi.

Bayan ƴan wani lokaci daga bayanin Tanko, mai taimaka wa Obi kan kafofin watsa labarai, Idris Zekeri, ya saki wani bayani yana ƙaryata rahotannin a matsayin ƙarya.

kwankwaso
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Namijin Ƙoƙarin Dakta Ɗantsoho Wajen Bunƙasa NPA Cikin Shekara Biyu Kacal

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.