A watan Yulin shekarar 2026, Shugaban Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Ƙasa, Abubakar Dakta Ɗantsoho ya cika shekaru biyu cif-cif, da naɗinsa, a muƙamin, wanda kuma tun bayan naɗin, ya ke ci gaba da kai gwauro da mari, wajen ƙara ciyar da hukumar ta NPA gaba.
Fannin na sufurin Jiragen Ruwan ƙasar dai, saboda rashin samar da tsare-tsare a shekarun baya, fannin ya kasance ana yin aiki da kayan da suka lalace da kuma yin aiki da kayan da na zamani ba.
Sai dai, wannan labarin a ƙarƙashin shugabancin Dakta Ɗantsoho, ya sauya duba da yadda ya yi amfani da ƙwarewar sa da kuma hazaƙarsa da ya ke da su a fannin kimiyyar zamani domin bunƙasa fannin. ta hanyar samar da kayan aiki na zamani a Tashoshin Jiragen Ruwan ƙasar
Kazalika, ya na ci gaba da bayar da gudunmawar gudunmawa, wajen ƙara haɓaka kuɗaɗen shiga ga hukumar ta NPA, musamman duba da yadda a 2026 kuɗaɗen shigar NPA, suka ƙaru zuwa Naira tiriliyan 1.489.
Wannan ƙarin kuɗaɗen shigar, ta nuna a zahiri, na irin gagarumar nasarar da Nijeriya ke ci gaba da bayarwa a fannin iya shugabanci na gari, a Afirka ta Yamma tare da kuma daƙile dukkan wata kafa, na zurarewar kuɗaɗen shiga, na gwamnatin ƙasar nan.
Samun nasarar da Dakta Ɗantsoho ya yi, musamman a ɓangaren ganin Gwamnatin Tarayya mai ci a ƙarƙashin shugabancin shugaban ƙasa Bola Tinubu ta amince da fitar da dala biliyan ɗaya domin gudanar da ayyukan zamantakewar da Tashoshin Jiragen Ruwan ƙasar, ba waramar ci gaba ne, aka samar ga fannin.
Bugu da ƙari, Dakta Ɗantsoho ya kasance kan gaba, wajen wanzar da tsarin bai ɗaya na ƙasa wato NSW, musamman bisa nufin magance duk wani ƙalubale da ya shafi cin hanci da rashawa, na gudanar da ayyuka, a Tashoshin Jiragen Ruwan ƙasar.
Akwai kuma aikin sabunta Tashoshin Apapa, Tin Can Island, Onne, da Kalaba, musamman domin ayyukansu, su yi daidai da hada-hadar kasuwanci ta duniya.
Haza zalika,wanzar kashi na ƙarshe na tsarin PCS da kuma amincewa da tsarin bai ɗaya na ƙasa NSW, hakan ya nuna yadda Dakta Ɗantsoho ya himmatu, na ganin ana yi amfani da tsari na zamani a tafiyar da ayyukan NPA tare da kuma ganin ana ci gaba da tabbatar da yin gaskiya da bin ƙa’idar da ta dace.
Bugu da ƙari, dabarun wanzar da manhajar da Dakta Ɗantsoho, musamman domin a samar da kyakyawan yanayi ga fannin, hakan ya bai wa masu gudanar da ayyuka a cikin ƙasar da sauran masu ruwa da tsaki a fannin, yin na’am, tare da kuma buƙatar, a rinƙa ci gaba da tattaunawa.
Wani abin dubi a nan shi ne, batun ci gaba da tattaunawa da masu ruwa da tsaki a fanin, ba wai batu ne na jeka nayi ka, amma batu ne, na shigo da ƙwararu a cikin harkar, domin ci gaba da haɓaka tsarin na tfiyar da ayyukan sufurin Jiragen Ruwan ƙasar, tare da kuma gudanar da hada-hada a fannin, ba tare da wata tangarɗa ba da kuma ƙara ci gaba da tara kuɗaɗen shiga.
Cif Ibrahim Nasiru, mazauni a Abuja, mai fashin baƙi ne, a al’amuran yau da kullum.














