Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kai hari unguwar Asase Ugbede da ke Naka, hedikwatar Gwer ta Yamma, a daren ranar Talata, inda suka kashe mutane biyu tare da jikkata wasu da dama.
Mazauna yankin sun ce maharan sun fito ne daga daji sannan suka fara harbe-harbe da misalin ƙarfe 8:30 na dare.
- Sabon Rikici Ya Kunno Kai A Jam’iyyar APC A Kano
- Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Taraktoci 2,000 Domin Noman Hekta Miliyan 1.5
Lamarin ya jefa al’umma cikin firgici.
Sojojin da ke kusa da yankin sun yi gaggawar kai ɗauki, abin da ya taimaka wajen rage yawan asarar rayuka.
Wani mazaunin yankin ya ce waɗanda suka rasu sun haɗa da malamin firamare Christopher Mule da matarsa.
Ya ƙara da cewa wata mata ta ji rauni kuma tana karɓar magani, yayin da sauran waɗanda suka samu raunuka aka duba su a asibiti tare da sallamar su.
Shugaban ƙaramar hukumar, Victor Ormin, ya tabbatar da faruwar harin, yana mai cewa jami’an tsaro na ci gaba da sintiri a yankin, kuma za a yi ƙarin bayani a nan gaba.















Discussion about this post