ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Taraktoci 2,000 Domin Noman Hekta Miliyan 1.5

by Sulaiman
4 months ago
Noma

Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da wasu sabbin taraktocin noma guda 2,000 domin bunkasa aikin noma na zamani a fadin kasar nan, tare da manufar noma sama da hekta miliyan 1.5 a duk shekara.

 

Ministan Noma da Samar da Abinci, Abubakar Kyari, ne ya bayyana hakan yayin bikin kaddamar da shirin a ranar Litinin a Abuja, inda ya ce wannan mataki wani gagarumin sauyi ne a bangaren noma karkashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

ADVERTISEMENT
  • Saka Ya Rattaba Hannu Akan Karin Kwantiragin Shekaru 5 A Arsenal 
  • Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Zamfara Saniyar Ware Wajen Tallafin Kuɗi Saboda Ba Ta APC – Dauda Lawal

A cewarsa, an kaddamar da shirin ne a karkashin shirin gwamnatin tarayya na Renewed Hope National Agricultural Mechanisation Programme, wanda zai samar da taraktoci masu karfin aiki tare da na’urorin noma sama da 9,000 domin inganta yawan amfanin gona.

 

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Ya bayyana cewa za a fara da tura taraktoci 600 a mataki na farko, sannan a biyo da wasu 750 da kuma 650 a matakai na gaba har a kai ga cika adadin 2,000 a fadin kasar nan baki daya.

 

Ministan ya kara da cewa ba za a bai wa mutane taraktocin a matsayin mallaka kai tsaye ba, sai dai za a mika su ga masu samar da ayyukan injinan noma (Mechanisation Service Providers), inda kowace na’ura za ta iya noma kusan hekta 600 a shekara.

 

Ana sa ran shirin zai taimaka wa manoma sama da miliyan 1.2 a duk fadin Najeriya, tare da inganta samar da abinci da kuma bunkasa tattalin arzikin karkara.

 

Hakazalika, ya ce gwamnatin ta samar da asusun tallafin noma na Naira biliyan 50 ta hannun Bankin Masana’antu domin saukaka harkokin zuba jari a fannin noma, yayin da aka kuma tanadi Naira biliyan 250 domin tallafa wa kananan manoma miliyan daya a daminar shekarar 2026.

 

Bugu da kari, gwamnatin ta shirya samar da motocin gyaran taraktoci guda 36, da kuma gina cibiyoyin kula da injinan noma guda bakwai a sassan kasar nan, tare da shirin kafa babbar masana’antar hada taraktoci da za ta rika samar da tsakanin guda 2,000 zuwa 4,000 a duk shekara.

 

Gwamnatin ta bayyana cewa wannan shiri zai taimaka wajen samar da ayyukan yi, rage wahalar aikin noma, da kuma kara yawan amfanin gona domin tabbatar da wadatar abinci a kasar nan.

Noma
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Next Post
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano

Ramadan: Kano Ta Bayar Da Umarnin Rufe Wuraren DJ Da Tarukan Nishaɗantarwa

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.