ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samar Da Motoci Masu Sulke: Ministan Tsaro Ya Yaba Da Jajircewar Gwamnan Zamfara A Fannin Tsaro

by Sulaiman
5 months ago
Zamfara

Ministan Tsaro na Ƙasa, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya yaba wa Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, bisa sayo motoci masu sulke, jiragen sa-ido marasa matuƙa (drones) da sauran kayan aiki domin ƙarfafa wa rundunonin tsaro a jihar.

 

A wani biki da aka gudanar a Gidan Gwamnati da ke Gusau ranar Laraba, Gwamna Lawal ya miƙa motoci 25 na zamani masu sulke (Armoured Personnel Carriers) ga jami’an tsaro, domin ƙara musu kariya yayin da suke gudanar da aiki a yankunan da ke da haɗarin tsaro a faɗin jihar.

ADVERTISEMENT
  1. Majalisar Jihar Ribas Ta Dakatar da Shirin Tsige Gwamnan Fubara
  2. Ramadan: An Nemi Al’umma Su Tausaya Wa Junansu

Sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa baya ga motocin sulken, gwamnatin Zamfara ta sayo jirgin sa ido mai ƙarfin shawagi na tsawon mita 80, wanda zai iya rufe nisan kilomita 50 tare da yin aiki na tsawon sa’o’i takwas ba tare da tsayawa ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Da yake jawabi a wajen ƙaddamar da kayayyakin, Gwamna Lawal ya ce halartar Ministan Tsaro ta ƙara nuna haɗin kai da fahimtar juna tsakanin Gwamnatin Tarayya da ta Zamfara wajen tabbatar da tsaro da doka a jihar.

 

Ya bayyana cewa tsawon shekaru, Zamfara ta fuskanci matsalar tsaro da ta kawo cikas ga rayuwar al’umma, noma, kasuwanci da zirga-zirga, lamarin da ya shafi tattalin arzikin jama’a.

 

Ya ce a karƙashin shirin “Rescue Mission”, gwamnatinsa ta koma daga martani na wucin-gadi zuwa tsarin gyara mai ɗorewa, inda aka kafa Asusun Tsaro na Jihar Zamfara domin samar da ingantaccen tallafin kayan aiki ga hukumomin tsaro. Haka kuma, an samar da rundunar tsaron al’umma, wato ‘Community Protection Guards’ bisa tanadin doka domin inganta tattara bayanan sirri da sama da tsaro.

 

Gwamnan ya ƙara da cewa, gwamnati ta raba motocin Hilux sabbi 150 ga jami’an tsaro da suka haɗa da ‘yan sanda, DSS da NSCDC, tare da sayo motocin Toyota Buffalo guda 20 – 10 masu sulke da 10 marasa sulke – da kuma babura sama da 600 domin saurin kai ɗauki a wuraren da ababen hawa ba sa iya shiga cikin sauƙi.

 

Ya jaddada cewa haɗa sa ido ta sama da ta ƙasa zai ƙara faɗaɗa hangen nesa na jami’an tsaro, inganta fahimtar yanayin wuri da kuma ƙarfafa daidaito tsakanin cibiyoyin umarni da jami’an da ke fagen daga.

 

A nasa bangaren, Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya ce matakin da gwamnatin Zamfara ta ɗauka na sayo motocin sulke da sauran kayan aiki ya nuna ƙwazon jagoranci da jajircewar gwamnan wajen kare rayuka da dukiyoyi.

 

Ya bayyana cewa, duk wani shugaba da ke zuba jari mai tsoka wajen tsaron jama’arsa yana aikewa da saƙo mai ƙarfi ga masu aikata laifi.

 

Ya ƙqra da cewa, kare rayuka da dukiyoyi ya wuce siyasa, yana mai nuna farin cikinsa da yadda gwamnatin Zamfara ta biya dukkan kuɗaɗen kayan aikin gaba ɗaya, lamarin da ke ƙara tabbatar da ƙudurin gwamnati na yaƙi da rashin tsaro.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC
  • Sulaiman
    Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji
  • Sulaiman
    Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

MASU ALAKA

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi
Manyan Labarai

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci
Manyan Labarai

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Next Post
Darussa Daga Ramadan Na (1)

Darussa Daga Ramadan Na (1)

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.