ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samar Da Motoci Masu Sulke: Ministan Tsaro Ya Yaba Da Jajircewar Gwamnan Zamfara A Fannin Tsaro

by Sulaiman
5 months ago
Zamfara

Ministan Tsaro na Ƙasa, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya yaba wa Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, bisa sayo motoci masu sulke, jiragen sa-ido marasa matuƙa (drones) da sauran kayan aiki domin ƙarfafa wa rundunonin tsaro a jihar.

 

A wani biki da aka gudanar a Gidan Gwamnati da ke Gusau ranar Laraba, Gwamna Lawal ya miƙa motoci 25 na zamani masu sulke (Armoured Personnel Carriers) ga jami’an tsaro, domin ƙara musu kariya yayin da suke gudanar da aiki a yankunan da ke da haɗarin tsaro a faɗin jihar.

ADVERTISEMENT
  1. Majalisar Jihar Ribas Ta Dakatar da Shirin Tsige Gwamnan Fubara
  2. Ramadan: An Nemi Al’umma Su Tausaya Wa Junansu

Sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa baya ga motocin sulken, gwamnatin Zamfara ta sayo jirgin sa ido mai ƙarfin shawagi na tsawon mita 80, wanda zai iya rufe nisan kilomita 50 tare da yin aiki na tsawon sa’o’i takwas ba tare da tsayawa ba.

 

LABARAI MASU NASABA

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

Da yake jawabi a wajen ƙaddamar da kayayyakin, Gwamna Lawal ya ce halartar Ministan Tsaro ta ƙara nuna haɗin kai da fahimtar juna tsakanin Gwamnatin Tarayya da ta Zamfara wajen tabbatar da tsaro da doka a jihar.

 

Ya bayyana cewa tsawon shekaru, Zamfara ta fuskanci matsalar tsaro da ta kawo cikas ga rayuwar al’umma, noma, kasuwanci da zirga-zirga, lamarin da ya shafi tattalin arzikin jama’a.

 

Ya ce a karƙashin shirin “Rescue Mission”, gwamnatinsa ta koma daga martani na wucin-gadi zuwa tsarin gyara mai ɗorewa, inda aka kafa Asusun Tsaro na Jihar Zamfara domin samar da ingantaccen tallafin kayan aiki ga hukumomin tsaro. Haka kuma, an samar da rundunar tsaron al’umma, wato ‘Community Protection Guards’ bisa tanadin doka domin inganta tattara bayanan sirri da sama da tsaro.

 

Gwamnan ya ƙara da cewa, gwamnati ta raba motocin Hilux sabbi 150 ga jami’an tsaro da suka haɗa da ‘yan sanda, DSS da NSCDC, tare da sayo motocin Toyota Buffalo guda 20 – 10 masu sulke da 10 marasa sulke – da kuma babura sama da 600 domin saurin kai ɗauki a wuraren da ababen hawa ba sa iya shiga cikin sauƙi.

 

Ya jaddada cewa haɗa sa ido ta sama da ta ƙasa zai ƙara faɗaɗa hangen nesa na jami’an tsaro, inganta fahimtar yanayin wuri da kuma ƙarfafa daidaito tsakanin cibiyoyin umarni da jami’an da ke fagen daga.

 

A nasa bangaren, Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya ce matakin da gwamnatin Zamfara ta ɗauka na sayo motocin sulke da sauran kayan aiki ya nuna ƙwazon jagoranci da jajircewar gwamnan wajen kare rayuka da dukiyoyi.

 

Ya bayyana cewa, duk wani shugaba da ke zuba jari mai tsoka wajen tsaron jama’arsa yana aikewa da saƙo mai ƙarfi ga masu aikata laifi.

 

Ya ƙqra da cewa, kare rayuka da dukiyoyi ya wuce siyasa, yana mai nuna farin cikinsa da yadda gwamnatin Zamfara ta biya dukkan kuɗaɗen kayan aikin gaba ɗaya, lamarin da ke ƙara tabbatar da ƙudurin gwamnati na yaƙi da rashin tsaro.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka
  • Sulaiman
    Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

MASU ALAKA

Zamfara
Manyan Labarai

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Manyan Labarai

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Zamfara
Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Next Post
Darussa Daga Ramadan Na (1)

Darussa Daga Ramadan Na (1)

LABARAI MASU NASABA

Zamfara

Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro

July 27, 2026
Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

July 27, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

July 27, 2026
Zamfara

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

July 27, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
Zamfara

WAFU B 2026: Nijeriya Ta Doke Ghana Da Ci 4-2 A Wasan Farko

July 27, 2026
An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

July 27, 2026
Zamfara

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.