ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samar Da Motoci Masu Sulke: Ministan Tsaro Ya Yaba Da Jajircewar Gwamnan Zamfara A Fannin Tsaro

by Sulaiman
7 months ago
Zamfara

Ministan Tsaro na Ƙasa, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya yaba wa Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, bisa sayo motoci masu sulke, jiragen sa-ido marasa matuƙa (drones) da sauran kayan aiki domin ƙarfafa wa rundunonin tsaro a jihar.

 

A wani biki da aka gudanar a Gidan Gwamnati da ke Gusau ranar Laraba, Gwamna Lawal ya miƙa motoci 25 na zamani masu sulke (Armoured Personnel Carriers) ga jami’an tsaro, domin ƙara musu kariya yayin da suke gudanar da aiki a yankunan da ke da haɗarin tsaro a faɗin jihar.

ADVERTISEMENT
  1. Majalisar Jihar Ribas Ta Dakatar da Shirin Tsige Gwamnan Fubara
  2. Ramadan: An Nemi Al’umma Su Tausaya Wa Junansu

Sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa baya ga motocin sulken, gwamnatin Zamfara ta sayo jirgin sa ido mai ƙarfin shawagi na tsawon mita 80, wanda zai iya rufe nisan kilomita 50 tare da yin aiki na tsawon sa’o’i takwas ba tare da tsayawa ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Da yake jawabi a wajen ƙaddamar da kayayyakin, Gwamna Lawal ya ce halartar Ministan Tsaro ta ƙara nuna haɗin kai da fahimtar juna tsakanin Gwamnatin Tarayya da ta Zamfara wajen tabbatar da tsaro da doka a jihar.

 

Ya bayyana cewa tsawon shekaru, Zamfara ta fuskanci matsalar tsaro da ta kawo cikas ga rayuwar al’umma, noma, kasuwanci da zirga-zirga, lamarin da ya shafi tattalin arzikin jama’a.

 

Ya ce a karƙashin shirin “Rescue Mission”, gwamnatinsa ta koma daga martani na wucin-gadi zuwa tsarin gyara mai ɗorewa, inda aka kafa Asusun Tsaro na Jihar Zamfara domin samar da ingantaccen tallafin kayan aiki ga hukumomin tsaro. Haka kuma, an samar da rundunar tsaron al’umma, wato ‘Community Protection Guards’ bisa tanadin doka domin inganta tattara bayanan sirri da sama da tsaro.

 

Gwamnan ya ƙara da cewa, gwamnati ta raba motocin Hilux sabbi 150 ga jami’an tsaro da suka haɗa da ‘yan sanda, DSS da NSCDC, tare da sayo motocin Toyota Buffalo guda 20 – 10 masu sulke da 10 marasa sulke – da kuma babura sama da 600 domin saurin kai ɗauki a wuraren da ababen hawa ba sa iya shiga cikin sauƙi.

 

Ya jaddada cewa haɗa sa ido ta sama da ta ƙasa zai ƙara faɗaɗa hangen nesa na jami’an tsaro, inganta fahimtar yanayin wuri da kuma ƙarfafa daidaito tsakanin cibiyoyin umarni da jami’an da ke fagen daga.

 

A nasa bangaren, Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya ce matakin da gwamnatin Zamfara ta ɗauka na sayo motocin sulke da sauran kayan aiki ya nuna ƙwazon jagoranci da jajircewar gwamnan wajen kare rayuka da dukiyoyi.

 

Ya bayyana cewa, duk wani shugaba da ke zuba jari mai tsoka wajen tsaron jama’arsa yana aikewa da saƙo mai ƙarfi ga masu aikata laifi.

 

Ya ƙqra da cewa, kare rayuka da dukiyoyi ya wuce siyasa, yana mai nuna farin cikinsa da yadda gwamnatin Zamfara ta biya dukkan kuɗaɗen kayan aikin gaba ɗaya, lamarin da ke ƙara tabbatar da ƙudurin gwamnati na yaƙi da rashin tsaro.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Darussa Daga Ramadan Na (1)

Darussa Daga Ramadan Na (1)

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.