Mai Martaba Sarkin Kano na 16, Alhaji Muhammadu Sanusi II, ya ce; Nijeriya na bukatar a gaggauta samar da dabaru da tsare-tsare na kasa, domin amfani da fasahohin da ke bullowa, musamman fasahar kere-kere, don samun ci gaba mai dorewa.
Sanusi ya bayyana haka ne, a wajen taron shekara 8 na kwamitin shugabannin jami’o’i mallakar jihohi a Nijeriya da aka gudanar a Kano.
“Wannan kasa tana bukatar dabaru da sabbin tsarin siyasa tare da bukatar kyakkyawan shiri, musamman a wannan karnin da muke ciki,” in ji shi.
Sarkin ya bukaci jami’o’in Nijeriya da su samar da taswirar fasahar zamani ta ‘AI’ na kasa, yana mai jaddada cewa; dole ne cibiyoyin su kasance kan gaba wajen koyarwa da bincike, domin tsara manufofin da ke kawo ci gaban kasa.
Har ila yau, ya yi gargadin cewa; Nijeriya na fuskantar barazanar samun koma baya, kamar sauran kasashe, ciki har da Ghana, da ta riga ta kirkiro tare da fara aiwatar da ingantattun dabarun AI da nufin horar da matasa, bunkasa bayanai da kuma sauyin tattalin arziki.
Sanusi II ya jaddada matsayin jami’o’i a matsayin ginshikan kungiyoyin farar hula, inda ya ce; dole ne cibiyoyin ilimi su ba da gudummawarsu wajen gabatar da jawaban kasa kan harkokin mulki, tattalin arziki, kimiyya da fasaha.
Ya kuma yaba wa gwamnatocin jihohi, bisa yadda suka fahimci muhimmancin shugabannin jami’o’in, wajen tsara alkiblar manufofi da kuma karfafa shugabanci a jami’o’i.
Tun da farko, Shugaban COPSUN, Ayodeji Omole, ya ce; taron ya nuna bukatar ci gaba da yin hadin gwiwa a tsakanin masu ruwa da tsaki, domin magance kalubalen da jami’o’in gwamnati ke fuskanta.
Haka zalika, ya yi nuni da cewa; tare da irin wadannan cibiyoyi sama da 60 a fadin kasar nan, yin aiki akai-akai, na da matukar muhimmanci wajen tabbatar da daidaiton manufofi da hada kan hukumomi da kuma inganta harkokin mulki.
Omole ya kara da cewa, dole ne jami’o’i su dace da abubuwan da suke faruwa a duniya, ciki har da ci gaban fasaha da kuma sauya bukatun tattalin arziki, ta hanyar kirkire-kirkire da tsare-tsare.
A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatansa, Suleiman Wali Sani, ya ce; gwamnatin jihar ta bai wa ilimi fifiko a matsayin babban ginshikin ci gaba.
Gwamnan ya ce, taron ya bayar da dama ga masu ruwa da tsaki, wajen samar da hanyoyin da za a bi domin inganta tsarin tafiyar da jami’o’i, kudade, kirkire-kirkire da kuma matakan ilimi.















Discussion about this post