ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarki Sanusi Ya Nemi Tinubu Ya Sauya Salon Tafiyar Da Mulkin Kasar Nan

by Sani Anwar
2 months ago
Sanusi

Mai Martaba Sarkin Kano na 16, Alhaji Muhammadu Sanusi II, ya ce; Nijeriya na bukatar a gaggauta samar da dabaru da tsare-tsare na kasa, domin amfani da fasahohin da ke bullowa, musamman fasahar kere-kere,  don samun ci gaba mai dorewa.

Sanusi ya bayyana haka ne, a wajen taron shekara 8 na kwamitin shugabannin jami’o’i mallakar jihohi a Nijeriya da aka gudanar a Kano.

“Wannan kasa tana bukatar dabaru da sabbin tsarin siyasa tare da bukatar kyakkyawan shiri, musamman a wannan karnin da muke ciki,” in ji shi.

ADVERTISEMENT

Sarkin ya bukaci jami’o’in Nijeriya da su samar da taswirar fasahar zamani ta ‘AI’ na kasa, yana mai jaddada cewa; dole ne cibiyoyin su kasance kan gaba wajen koyarwa da bincike, domin tsara manufofin da ke kawo ci gaban kasa.

Har ila yau, ya yi gargadin cewa; Nijeriya na fuskantar barazanar samun koma baya, kamar sauran kasashe, ciki har da Ghana, da ta riga ta kirkiro tare da fara aiwatar da ingantattun dabarun AI da nufin horar da matasa, bunkasa bayanai da kuma sauyin tattalin arziki.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Sanusi II ya jaddada matsayin jami’o’i a matsayin ginshikan kungiyoyin farar hula, inda ya ce; dole ne cibiyoyin ilimi su ba da gudummawarsu wajen gabatar da jawaban kasa kan harkokin mulki, tattalin arziki, kimiyya da fasaha.

Ya kuma yaba wa gwamnatocin jihohi, bisa yadda suka fahimci muhimmancin shugabannin jami’o’in, wajen tsara alkiblar manufofi da kuma karfafa shugabanci a jami’o’i.

Tun da farko, Shugaban COPSUN, Ayodeji Omole, ya ce; taron ya nuna bukatar ci gaba da yin hadin gwiwa a tsakanin masu ruwa da tsaki, domin magance kalubalen da jami’o’in gwamnati ke fuskanta.

Haka zalika, ya yi nuni da cewa; tare da irin wadannan cibiyoyi sama da 60 a fadin kasar nan, yin aiki akai-akai, na da matukar muhimmanci wajen tabbatar da daidaiton manufofi da hada kan hukumomi da kuma inganta harkokin mulki.

Omole ya kara da cewa, dole ne jami’o’i su dace da abubuwan da suke faruwa a duniya, ciki har da ci gaban fasaha da kuma sauya bukatun tattalin arziki, ta hanyar kirkire-kirkire da tsare-tsare.

A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatansa, Suleiman Wali Sani, ya ce; gwamnatin jihar ta bai wa ilimi fifiko a matsayin babban ginshikin ci gaba.

Gwamnan ya ce, taron ya bayar da dama ga masu ruwa da tsaki, wajen samar da hanyoyin da za a bi domin inganta tsarin tafiyar da jami’o’i, kudade, kirkire-kirkire da kuma matakan ilimi.

Sanusi
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Amince Da Kaya Na Farko Da Aka Shigo Da Su A Karkashin Manufar Soke Haraji Ga Kayayyakin Afirka

Kasar Sin Ta Amince Da Kaya Na Farko Da Aka Shigo Da Su A Karkashin Manufar Soke Haraji Ga Kayayyakin Afirka

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026
Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.