ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarki Sanusi Ya Nemi Tinubu Ya Sauya Salon Tafiyar Da Mulkin Kasar Nan

by Sani Anwar
1 month ago
Sanusi

Mai Martaba Sarkin Kano na 16, Alhaji Muhammadu Sanusi II, ya ce; Nijeriya na bukatar a gaggauta samar da dabaru da tsare-tsare na kasa, domin amfani da fasahohin da ke bullowa, musamman fasahar kere-kere,  don samun ci gaba mai dorewa.

Sanusi ya bayyana haka ne, a wajen taron shekara 8 na kwamitin shugabannin jami’o’i mallakar jihohi a Nijeriya da aka gudanar a Kano.

“Wannan kasa tana bukatar dabaru da sabbin tsarin siyasa tare da bukatar kyakkyawan shiri, musamman a wannan karnin da muke ciki,” in ji shi.

ADVERTISEMENT

Sarkin ya bukaci jami’o’in Nijeriya da su samar da taswirar fasahar zamani ta ‘AI’ na kasa, yana mai jaddada cewa; dole ne cibiyoyin su kasance kan gaba wajen koyarwa da bincike, domin tsara manufofin da ke kawo ci gaban kasa.

Har ila yau, ya yi gargadin cewa; Nijeriya na fuskantar barazanar samun koma baya, kamar sauran kasashe, ciki har da Ghana, da ta riga ta kirkiro tare da fara aiwatar da ingantattun dabarun AI da nufin horar da matasa, bunkasa bayanai da kuma sauyin tattalin arziki.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Sanusi II ya jaddada matsayin jami’o’i a matsayin ginshikan kungiyoyin farar hula, inda ya ce; dole ne cibiyoyin ilimi su ba da gudummawarsu wajen gabatar da jawaban kasa kan harkokin mulki, tattalin arziki, kimiyya da fasaha.

Ya kuma yaba wa gwamnatocin jihohi, bisa yadda suka fahimci muhimmancin shugabannin jami’o’in, wajen tsara alkiblar manufofi da kuma karfafa shugabanci a jami’o’i.

Tun da farko, Shugaban COPSUN, Ayodeji Omole, ya ce; taron ya nuna bukatar ci gaba da yin hadin gwiwa a tsakanin masu ruwa da tsaki, domin magance kalubalen da jami’o’in gwamnati ke fuskanta.

Haka zalika, ya yi nuni da cewa; tare da irin wadannan cibiyoyi sama da 60 a fadin kasar nan, yin aiki akai-akai, na da matukar muhimmanci wajen tabbatar da daidaiton manufofi da hada kan hukumomi da kuma inganta harkokin mulki.

Omole ya kara da cewa, dole ne jami’o’i su dace da abubuwan da suke faruwa a duniya, ciki har da ci gaban fasaha da kuma sauya bukatun tattalin arziki, ta hanyar kirkire-kirkire da tsare-tsare.

A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatansa, Suleiman Wali Sani, ya ce; gwamnatin jihar ta bai wa ilimi fifiko a matsayin babban ginshikin ci gaba.

Gwamnan ya ce, taron ya bayar da dama ga masu ruwa da tsaki, wajen samar da hanyoyin da za a bi domin inganta tsarin tafiyar da jami’o’i, kudade, kirkire-kirkire da kuma matakan ilimi.

Sanusi
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Amince Da Kaya Na Farko Da Aka Shigo Da Su A Karkashin Manufar Soke Haraji Ga Kayayyakin Afirka

Kasar Sin Ta Amince Da Kaya Na Farko Da Aka Shigo Da Su A Karkashin Manufar Soke Haraji Ga Kayayyakin Afirka

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.