ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarki Sanusi Ya Nemi Tinubu Ya Sauya Salon Tafiyar Da Mulkin Kasar Nan

by Sani Anwar
3 months ago
Sanusi

Mai Martaba Sarkin Kano na 16, Alhaji Muhammadu Sanusi II, ya ce; Nijeriya na bukatar a gaggauta samar da dabaru da tsare-tsare na kasa, domin amfani da fasahohin da ke bullowa, musamman fasahar kere-kere,  don samun ci gaba mai dorewa.

Sanusi ya bayyana haka ne, a wajen taron shekara 8 na kwamitin shugabannin jami’o’i mallakar jihohi a Nijeriya da aka gudanar a Kano.

“Wannan kasa tana bukatar dabaru da sabbin tsarin siyasa tare da bukatar kyakkyawan shiri, musamman a wannan karnin da muke ciki,” in ji shi.

ADVERTISEMENT

Sarkin ya bukaci jami’o’in Nijeriya da su samar da taswirar fasahar zamani ta ‘AI’ na kasa, yana mai jaddada cewa; dole ne cibiyoyin su kasance kan gaba wajen koyarwa da bincike, domin tsara manufofin da ke kawo ci gaban kasa.

Har ila yau, ya yi gargadin cewa; Nijeriya na fuskantar barazanar samun koma baya, kamar sauran kasashe, ciki har da Ghana, da ta riga ta kirkiro tare da fara aiwatar da ingantattun dabarun AI da nufin horar da matasa, bunkasa bayanai da kuma sauyin tattalin arziki.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Sanusi II ya jaddada matsayin jami’o’i a matsayin ginshikan kungiyoyin farar hula, inda ya ce; dole ne cibiyoyin ilimi su ba da gudummawarsu wajen gabatar da jawaban kasa kan harkokin mulki, tattalin arziki, kimiyya da fasaha.

Ya kuma yaba wa gwamnatocin jihohi, bisa yadda suka fahimci muhimmancin shugabannin jami’o’in, wajen tsara alkiblar manufofi da kuma karfafa shugabanci a jami’o’i.

Tun da farko, Shugaban COPSUN, Ayodeji Omole, ya ce; taron ya nuna bukatar ci gaba da yin hadin gwiwa a tsakanin masu ruwa da tsaki, domin magance kalubalen da jami’o’in gwamnati ke fuskanta.

Haka zalika, ya yi nuni da cewa; tare da irin wadannan cibiyoyi sama da 60 a fadin kasar nan, yin aiki akai-akai, na da matukar muhimmanci wajen tabbatar da daidaiton manufofi da hada kan hukumomi da kuma inganta harkokin mulki.

Omole ya kara da cewa, dole ne jami’o’i su dace da abubuwan da suke faruwa a duniya, ciki har da ci gaban fasaha da kuma sauya bukatun tattalin arziki, ta hanyar kirkire-kirkire da tsare-tsare.

A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatansa, Suleiman Wali Sani, ya ce; gwamnatin jihar ta bai wa ilimi fifiko a matsayin babban ginshikin ci gaba.

Gwamnan ya ce, taron ya bayar da dama ga masu ruwa da tsaki, wajen samar da hanyoyin da za a bi domin inganta tsarin tafiyar da jami’o’i, kudade, kirkire-kirkire da kuma matakan ilimi.

Sanusi
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Amince Da Kaya Na Farko Da Aka Shigo Da Su A Karkashin Manufar Soke Haraji Ga Kayayyakin Afirka

Kasar Sin Ta Amince Da Kaya Na Farko Da Aka Shigo Da Su A Karkashin Manufar Soke Haraji Ga Kayayyakin Afirka

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.