A Jiya Litinin ne ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Sevilla da ke buga gasar Laliga ta ƙasar Sifaniya, ta sanar da korar kocinta Matias Almeyda, yayin da zakarun na gasar Europa League sau bakwai suka tsinci kansu a matsayi na 15 a teburin gasar.
Ƙungiyar ta yankin Andalus, yanzu haka maki uku ne kacal ya rage tsakaninta da Mallorca wadda ke matsayi na 18.
- Kwamishinan Ilimi Na Zamfara Madawaki Ya Yi Murabus Daga Muƙaminsa
- APC Ta Bayyana Shirin Taron Ƙasa Don Zaɓen 2027 — Masari
Sevilla ta fitar da wata gajeriyar sanarwa dangane da korar kocin nata, inda ta gode wa tsohon ɗan wasan na tawagar Argentina mai shekaru 52, tare da yi masa fatan nasara.
Sanarwar ta ruwaito cewa “An sauke Matias Almeyda daga aikinsa na matsayin kocin tawagar farko ta Sevilla FC.
“Sevilla FC na gode wa Matias Almeyda da tawagarsa saboda ƙoƙarinsa da ƙwarewarsa da kuma yi masa fatan alheri a duk inda ya tsinci kanshi a nan gaba.”
Sai dai sanarwar ba ta ambaci wanda zai maye gurbinsa ko kuma wanda zai iya zama kocin wucin gadi ba bayan kammala hutun ƙasa da ƙasa nan da makonni biyu masu zuwa.
Almeyda, wanda ya fara aikinsa na horarwa a River Plate a shekarar 2011, ya jagoranci AEK Athens daga shekarar 2022 zuwa 2025 kafin Sevilla ta ɗauke shi a kwantiragin shekaru uku.















Discussion about this post