ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarwari 40 Zuwa Ga Uwargida (1)

by Bilkisu Tijjani
3 months ago
40

1. Kalmar uwargida ita ce macen farko wanda aka fara aura, duk wacce za ta zo sai dai ta shigo a ta biyu ko a ta uku har ma ta huɗu, amma wannan uwargidan ke ce macen farko.

2. A matsayinki na uwargida ke za ki fara gina tubalin rayuwar aurenki, ke ce za ki fara tsara yadda zaman ku zai kasance tare da mijin naki saboda da yawa matar farko ita ce makarantan farko ga rayuwar namiji.

3. Ki kula da ibada domin shi ne tushen komai, ibada ɗajin tsoron Ubangiji ki san cewa dukkan abin da za ki yi koda a ɓoye ne, idan kin ɓoye wa mijinki lallai baki isa ki ɓoye wa Ubangiji ba.

ADVERTISEMENT
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci Matasa Su Riƙa Tantance Sahihancin Labari Kafin Su Yaɗa Shi
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci Matasa Su Riƙa Tantance Sahihancin Labari Kafin Su Yaɗa Shi

4. Haƙuri da kawaici dole ne ki zama hakan domin zaman rayuwar aure ɓangaren haƙuri shi ne babban jigo a cikin aure, idan ba ki da haƙuri komai zaina faruwa shi ya sa ake son uwargida ki zama mai haƙuri.

5. Ladabi da biyayya matuƙar ba ki da wannan, tsaf mijinki za ki fita daga zuciyar sa, ki sani cewa mijinki shugaba ne a gare ki ki masa ladabi da biyayya, matuƙar abin da ya umurce ki bai kauce wa addini ba.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

6. Karki mallaki mijinki ta hanyar sihiri, za ki hallaka kuma ranan gobe ƙiyama wuta ta zama makomar ki.

7. Kar ki je wurin wani boka domin neman biyan buƙata, idan ba ki gane kan mijin ki ba, ki hana idonki barci ki kai wa Ubangiji kukanki cikin dare za ki ga dukkan al’amuran ki sun warware miki.

8. Ki kula da tsaftar cikin gidanki, yaranki, mijinki. Domin tsabta aba ce mai kyau kuma yana daga cikin musulunci, idan kika zama ƙazamar mace kenan wulakanci bibbiyu za ki fuskanta.

9. Iya girki yana daga cikin makamin dake sace zuciyar namiji, idan kika iya girki za ki mallaki mijinki kuma kin wuce raini a wajansa.

10. Iyayen mijinki, ki kula dasu ki basu girmansu, ki kyautata masu koda kin lura da mijinki baida niyyan masu abu, ke kiyi amfani da damar ki ki saka ya masu abu, za ki iya yi musu kyauta daidai ƙarfinki, ki faranta masu koda ba waje ɗaya kuke da su ba, saboda sun gama yi miki komai da suka haifi abin da kika aura.

11. Ki iya zauna da dangin mijinki lafiya, idan sun zo wajenki ki kula da su, idan wani abu ya faru ki je masu idan na murna ne ki taya su, idan kuma na baƙin ciki ne shi ma ki taya su ki zauna da su lafiya.

12. Kar ki zama wata ballagazar mace mara sanin mutuncin kanta.

13. Duk rintsi ki riƙa kulawa da gyaran jikinki ba wai ko wane irin takarkace za ki yi amfani da shi wurin gyaran jiki ba, idan ba ki kula ba da hakan sai ya zamar miki matsala a nan gaba, ki sani kar ki bari mijinki ji wani wari a jikinki, ki kula ta wannan ɓangaren da kyau. 14. Ki zama mace da ta iya ado da kwalliya.

15. Duk bayan sati biyu ko kwana goma ki je kitso mai kyau, ki lura da abin da mijinki ya fi so, wani na son ganin matarsa da kitso, wani kuma ya fi son ganin gashin ta haka a gyare.

16. Kar ki zama mai mummunan lafuza ga mijinki, uwargida ki san irin lafuzan da za yi amfani da shi wurin magana da mijinki. 17. Ko ki san cewa uwargida maza suna son macen da ta iya kalamai mai daɗi?

Saboda haka kema ki iya idan ma ba ki iya ba, ki koya ga zamanin Soshiyal midiya. Musamman guruf ɗin mata ana wayar da kai ki tambaya za a koya miki.

Za mu Ci Gaba Mako Mai Zuwa Idan Allah Ya Kai Mu

 

40
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasihar Da Ya Dace Dukkan Iyaye Su Yi Wa ‘Yaƴansu Yayin  Aure?
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa

MASU ALAKA

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya
Rahotonni

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati
Labarai

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare
Labarai

Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare

June 12, 2026
Next Post
40

Nazari Kan Dabarun Shuka Mangoro A Zamanance

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.