ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci Matasa Su Riƙa Tantance Sahihancin Labari Kafin Su Yaɗa Shi

by Shehu Yahaya and Sulaiman
3 months ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya gargaɗi cewa yaɗa labaran ƙarya yana haifar da babbar barazana ga ɗabi’a da haɗin kan ƙasa, inda ya yi kira ga matasan Nijeriya da su riƙa tabbatar da sahihancin duk wani labari kafin su yaɗa shi.

 

Ministan ya bayyana hakan ne yayin Laccar Ramadana ta Haɗin Gwiwa karo na 20 wadda Hukumar Talbijin ta Nijeriya (NTA), Hukumar Rediyon Tarayyar Nijeriya (FRCN) da gidan rediyon Muryar Nijeriya (VON) suka shirya a Kaduna.

ADVERTISEMENT
  • Jami’ar Osun Ta Buƙaci Wani Kamfani Ya Janye Kalamansa Kan Batun Ma’aikatan Bogi A Jami’ar
  • Ban Fuskanci Matsala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Asiya Muhammad

Ya yi gargaɗin cewa amfani da kafafen sadarwa ta hanyar da ba ta dace ba yana iya ƙara rarrabuwar kawuna da raunana haɗin kan ƙasa.

 

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

A cewar sa, duk da cewa fasahar zamani ta kawo damammaki masu yawa, tana kuma zuwa da ƙalubalen ɗabi’a da ke buƙatar ladabi da ɗaukar alhaki.

 

Idris ya ce tantance sahihancin labari ya zama wajibi na ɗan ƙasa da kuma nauyin ɗabi’a a wannan zamani, yana mai cewa, “Sanin yadda kafofin watsa labarai suke aiki shi ne rigakafin yaɗuwar labaran ƙarya.”

 

Ministan ya buƙaci matasa da su yi amfani da kafafen dijital wajen neman ilimi, ƙirƙire-ƙirƙire da bunƙasa ƙasa, maimakon haifar da rarrabuwa.

 

Ya ƙara da cewa: “Ku tantance kafin ku yaɗa. Ku dakata. Ku binciki tushe,” yana mai jaddada cewa wajibi ne a yi amfani da fasahar zamani wajen ƙarfafa haɗin kai da cigaba.

 

Ya jaddada cewa yawan matasan Nijeriya na daga cikin manyan ƙarfin ta, amma makomar ƙasa tana dogara da yadda ake jagorantar su da tallafa masu.

 

Ya ce: “Ƙasar da ta kasa kula da matasan ta ba ta da makoma. Muna saka hannun jari a tsarin da zai mayar da fasahar dijital matattakalar samun damarmaki.”

 

Ministan ya bayyana cewa gwamnati tana aiwatar da shirye-shiryen tallafa wa matasa da dama a ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ciki har da shirin 3MTT, Lamunin Ilimi na Nijeriya (NELFUND), da kuma kafa cibiyar farko a Afrika ta koyar da ilimin kafofin watsa labarai.

 

Haka kuma, Ministan ya ambaci amincewar da UNESCO ta bai wa Nijeriya ta karɓar baƙuncin cibiyar farko a Afrika ta Ilimin Kafofin Watsa Labarai (IMILI), yana mai cewa wannan wani muhimmin mataki ne wanda zai taimaka wajen horar da jama’a kan tunani mai zurfi domin guje wa ruɗin labarai.

 

Ya nanata cewa kare ɗabi’a da sararin labarai ba aikin gwamnati kaɗai ba ne, yana kira ga iyaye, malamai, shugabannin addini, ‘yan jarida da matasa da su haɗa kai wajen gina al’umma mai fasaha da ɗabi’a tagari.

 

Laccar ta bana ta samu halartar gwamnonin jihohi da manyan jami’an gwamnati da sarakunan gargajiya da shugabannin kafafen yaɗa labarai daga sassa daban-daban na ƙasar nan.

Minista
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Bayan Shehu Sani Ya Ƙalubalanci Zailani, Rikicin APC Ya Ƙara Zafi A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ya Dace ‘Yan Arewa Su Ƙara Marawa Tinubu Baya Domin Kammala Wa’adi Na Biyu — Shehu Sani
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Zargin Ware Ɓangaren El-rufa’i: Rikicin Cikin Gida Ya Kaure A Jam’iyyar ADC, Kaduna
Minista
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Shawarwari 40 Zuwa Ga Uwargida   (1)

Shawarwari 40 Zuwa Ga Uwargida (1)

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.