ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sheikh Zakzaky Ya Halarci Addu’ar Bakwai Ta Rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi 

Duk Duniya Babu Malamin Da Ke Tafsiri Babu Littafi Sai Shaikh Dahiru Usman, In Ji Al-Zakzaky

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
7 months ago
Zakzaky

A ranar Alhamis jagoran ‘yan uwa Musulmai a Nijeriya da aka fi sani da Shi’a, Shaikh Ibraheem Zakzaky ya halarci addu’ar kwanaki bakwai na rasuwar fitaccen malamin addinin Musulunci, Shaikh Dahiru Usman Bauchi tare da miƙa cikakken ta’aziyyarsa ga iyalai da almajiran marigayin.

 

Ta’aziyyar wacce ta gudana a Masallacin marigayin da ke unguwar Makera a cikin garin Bauchi, Ƙani kuma shaƙiƙin Shaikh Zakzaky, Malam Badamasi Yaqoub da babban ɗansa, Muhammad Zakzaky tare da wasu malamai ne suka wakilci Malam Zakzaky.

ADVERTISEMENT
  • Duniya Za Ta Kara Kyau In Ba A Nuna Fin Karfi
  • Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 74, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace 318 A Watan Nuwamba 

Da ya ke miƙa ta’aziyya a madadin Shaikh Zakzaky, Malam Badamasi Yaqoub, ya ce duniya ce ta yi rashin babban bango wanda ya hidimta wa addinin Musulunci.

 

LABARAI MASU NASABA

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Ya ce: “Muna jaddada gaisuwa ga iyalai, ɗaliban Shehu Dahiru Bauchi, ba ɗaliban ba kawai ba har ma da al’ummar duniya baki ɗaya domin rashin Shehu Dahiru Bauchi kamar rashi ne da duniya ta yi. Domin kamar wani bango ne gaba ɗaya. Mahaddaccin Alkur’ani wanda babu kamar irinsa, wanda ya zo da shigen tafsiri wanda a duniya ba a ga mai tafsiri irinsa ba; wanda ya ke fassara Kur’ani da abin da ke ƙwaƙwalwarsa ba tare da ya duba komai ba.’

 

Ya ƙara da cewa, dukkanin bayani da fassara tare da hadisai da Shaikh Dahiru ke kwararowa da kai ya ke yinsu ba tare da ya sanya littafi a gabansa ba, ya ce babu kamarsa a duk duniya.

 

Ya ƙara da nuna irin gudunmawar da marigayin ya bai wa addinin Musulunci, “Ko ka ƙi ko ka so Sheikh Dahiru Bauchi ya taimakeka ko kana ɓangarensa ko ba ka ɓangarensa, Sheikh Dahiru Bauchi Malaminka ne. Domin Malamin Kur’ani ne. Allah ya yi masa rahama.”

 

“Muna jaddada gaisuwa gareku (iyalai) gaba ɗaya bisa wannan babban rashi. Allah ya masa rahama.”

 

Ya ce bisa babban rashin da jimamin wannan rashin da aka yi ne ya sana jagoran harƙa musulunci Shaikh Malam Ibraheem Yaqoub Al-Zakzaky ya turo shaƙiƙansa da iyalansa domin su zo su yi wa iyalan Shehu Dahiru Bauchi ta’aziyya.

 

Ya yi addu’ar Allah ya jikanshi ya haramsheshi, Allah ya sa ya huta Allah ya kaddara rayuwarshi na lahira ya fi masa na duniya alkairi. Allah sa kabarinsa ya zama rauda fil riyadul Jannah.

 

Da ya ke amsar ta’aziyyar, Khalifa Shaikh Ibrahim Dahiru Usman Bauchi, ya nuna godiyarsu ga ta’aziyyar, tare da bayyana rashin Shehin a matsayin abin yi ta’aziyya wa juna gaba daya. Ya bayyana irin kyakkyawar alakar da ke tsakanin Shaikh Ibraheem Zakzaky da marigayi Shaikh Dahiru Bauchi, inda ya bada misali da irin lokutan da Shaikh Zakzaky ya rika ziyartan Shehi a baya, har Shehi kan gabatar da shi ya ja su Sallah.

 

“Mun gode da wannan ta’aziyyar, Amma ta’aziyyar namu ne dukka. Shaikh Ibraheem Al-Zakzaky ba bako ba ne a wannan gidan ina ji lokacin da ya ke zuwa ziyara (wajen magariyi) yawanci in ya zo ma Shehi ya na sa shi ya jagorancemu sallah, to Allah ya saka musu da alkairi, Allah ya daukaka addinin musulunci.

 

Khalifan Shehin ya yi adduar Allah ya ɗauka musulunci da musulmai ya ƙara haɗa kan al’ummar ƙasar nan baki daya.

 

Idan za a tuna dai Shaikh Dahiru ya rasu ne da safiyar ranar Alhamis inda ya ke cika kwanaki bakwai da rasuwar. An gudanar da addu’o’i na musamman da nufin Allah ya gafarta wa mamacin. Ɓangarori daban-daban ne suke ci gaba da ta’aziyyarsu.

Zakzaky
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
Zakzaky
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
Next Post
Binciken Ra’ayoyi Na CGTN: Sin Ta Bukaci Japan Ta Janye Katobararta

Binciken Ra’ayoyi Na CGTN: Sin Ta Bukaci Japan Ta Janye Katobararta

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.