ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sheikh Zakzaky Ya Halarci Addu’ar Bakwai Ta Rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi 

Duk Duniya Babu Malamin Da Ke Tafsiri Babu Littafi Sai Shaikh Dahiru Usman, In Ji Al-Zakzaky

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
6 months ago
Zakzaky

A ranar Alhamis jagoran ‘yan uwa Musulmai a Nijeriya da aka fi sani da Shi’a, Shaikh Ibraheem Zakzaky ya halarci addu’ar kwanaki bakwai na rasuwar fitaccen malamin addinin Musulunci, Shaikh Dahiru Usman Bauchi tare da miƙa cikakken ta’aziyyarsa ga iyalai da almajiran marigayin.

 

Ta’aziyyar wacce ta gudana a Masallacin marigayin da ke unguwar Makera a cikin garin Bauchi, Ƙani kuma shaƙiƙin Shaikh Zakzaky, Malam Badamasi Yaqoub da babban ɗansa, Muhammad Zakzaky tare da wasu malamai ne suka wakilci Malam Zakzaky.

ADVERTISEMENT
  • Duniya Za Ta Kara Kyau In Ba A Nuna Fin Karfi
  • Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 74, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace 318 A Watan Nuwamba 

Da ya ke miƙa ta’aziyya a madadin Shaikh Zakzaky, Malam Badamasi Yaqoub, ya ce duniya ce ta yi rashin babban bango wanda ya hidimta wa addinin Musulunci.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Ya ce: “Muna jaddada gaisuwa ga iyalai, ɗaliban Shehu Dahiru Bauchi, ba ɗaliban ba kawai ba har ma da al’ummar duniya baki ɗaya domin rashin Shehu Dahiru Bauchi kamar rashi ne da duniya ta yi. Domin kamar wani bango ne gaba ɗaya. Mahaddaccin Alkur’ani wanda babu kamar irinsa, wanda ya zo da shigen tafsiri wanda a duniya ba a ga mai tafsiri irinsa ba; wanda ya ke fassara Kur’ani da abin da ke ƙwaƙwalwarsa ba tare da ya duba komai ba.’

 

Ya ƙara da cewa, dukkanin bayani da fassara tare da hadisai da Shaikh Dahiru ke kwararowa da kai ya ke yinsu ba tare da ya sanya littafi a gabansa ba, ya ce babu kamarsa a duk duniya.

 

Ya ƙara da nuna irin gudunmawar da marigayin ya bai wa addinin Musulunci, “Ko ka ƙi ko ka so Sheikh Dahiru Bauchi ya taimakeka ko kana ɓangarensa ko ba ka ɓangarensa, Sheikh Dahiru Bauchi Malaminka ne. Domin Malamin Kur’ani ne. Allah ya yi masa rahama.”

 

“Muna jaddada gaisuwa gareku (iyalai) gaba ɗaya bisa wannan babban rashi. Allah ya masa rahama.”

 

Ya ce bisa babban rashin da jimamin wannan rashin da aka yi ne ya sana jagoran harƙa musulunci Shaikh Malam Ibraheem Yaqoub Al-Zakzaky ya turo shaƙiƙansa da iyalansa domin su zo su yi wa iyalan Shehu Dahiru Bauchi ta’aziyya.

 

Ya yi addu’ar Allah ya jikanshi ya haramsheshi, Allah ya sa ya huta Allah ya kaddara rayuwarshi na lahira ya fi masa na duniya alkairi. Allah sa kabarinsa ya zama rauda fil riyadul Jannah.

 

Da ya ke amsar ta’aziyyar, Khalifa Shaikh Ibrahim Dahiru Usman Bauchi, ya nuna godiyarsu ga ta’aziyyar, tare da bayyana rashin Shehin a matsayin abin yi ta’aziyya wa juna gaba daya. Ya bayyana irin kyakkyawar alakar da ke tsakanin Shaikh Ibraheem Zakzaky da marigayi Shaikh Dahiru Bauchi, inda ya bada misali da irin lokutan da Shaikh Zakzaky ya rika ziyartan Shehi a baya, har Shehi kan gabatar da shi ya ja su Sallah.

 

“Mun gode da wannan ta’aziyyar, Amma ta’aziyyar namu ne dukka. Shaikh Ibraheem Al-Zakzaky ba bako ba ne a wannan gidan ina ji lokacin da ya ke zuwa ziyara (wajen magariyi) yawanci in ya zo ma Shehi ya na sa shi ya jagorancemu sallah, to Allah ya saka musu da alkairi, Allah ya daukaka addinin musulunci.

 

Khalifan Shehin ya yi adduar Allah ya ɗauka musulunci da musulmai ya ƙara haɗa kan al’ummar ƙasar nan baki daya.

 

Idan za a tuna dai Shaikh Dahiru ya rasu ne da safiyar ranar Alhamis inda ya ke cika kwanaki bakwai da rasuwar. An gudanar da addu’o’i na musamman da nufin Allah ya gafarta wa mamacin. Ɓangarori daban-daban ne suke ci gaba da ta’aziyyarsu.

Zakzaky
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba
Zakzaky
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Binciken Ra’ayoyi Na CGTN: Sin Ta Bukaci Japan Ta Janye Katobararta

Binciken Ra’ayoyi Na CGTN: Sin Ta Bukaci Japan Ta Janye Katobararta

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.