ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Raya Kasar Sin Karo Na 15, Taswirar Ci Gaban Kasashen Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Sin

Mataimakin daraktan ofishin kula da harkokin kudi da tattalin arziki na kwamitin kolin JKS Han Wenxiu ya bayyana yayin taro kan ci gaban kasar Sin na 2026 da aka yi jiya cewa, kasar za ta ci gaba da kara wa tattalin arzikin duniya tabbaci da daidaito da kuzari. Ko ta yaya za ta yi hakan?

A baya bayan nan, ana samun kafafen yada labarai na yammacin duniya da ke hasashen kasar Sin ba za ta cimma burinta na habakar tattalin arziki ba, suna ganin yanayin Gabas ta Tsakiya zai rage karfinta na fitar da kayayyaki. Abun lura shi ne, dogaron da tattalin arzikin Sin ke yi kan gudunmawar bangaren fitar da kayyayaki zuwa ketare, ya ragu daga kaso 59.2 a shekarar 2008, zuwa kaso 32.7 a bara. A yanzu kasar Sin ta fi mayar da hankali ne kan habaka kasuwar cikin gida, maimakon dogaro da fitar da kayayyaki waje kawai, inda wannan bangare ya bayar da gudunmawar da ta kai kaso 63.7 ga tattalin arzikin kasar a bara.

  • Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Tarwatsa Gada A Neja Domin Daƙile Harin Sojoji
  • Benin Ta Gudanar Da Bikin Ranar Taijiquan Ta Duniya A Karon Farko 

Irin wadannan alkaluma suna kara nuna kaifin basira da hangen nesa na kasar Sin, Shi ya sa shirinta na raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 15 da aka fara a bana, ke zaman wata sabuwar hanya da sassan duniya za su ci gajiya. A ganina, shirin bai tsaya kan raya kasar Sin kadai ba, shiri ne na Sin na tafiya tare da kasa da kasa kan tafarkin ci gaba.

ADVERTISEMENT

A matsayinta na kasa ta biyu mafi karfin tattalin arziki, kwanciyar hankali da daidaton tattalin arzikinta na da matukar muhimmanci ga tattalin arzikin duniya. Kuma cikin shirin, kasar Sin mai bayar da gudunmawar kaso 30 ga tattalin arzikin duniya, na da burin ci gaba da rike kambunta, ta hanyoyin bunkasa bukatu na cikin gida da habaka bude kasuwarta ga kasashen waje da tunkarar kalubale. Mun ga yadda tasirin COVID-19 ya lalata tattalin arzikin kasashen duniya, amma kuma saboda tubala masu kwari na tattalin arzikin kasar, ba ta yi fama da tasirin kamar sauran kasashe ba.

Maimakon rufe kofofi ko takaita cinikayya da kasashen duniya, kasar Sin za ta kara fadada bude kofofinta da ma rage shingayen dake tarnaki ga cinikayya tsakaninta da kasashen duniya, domin ba su damar cin gajiyar babbar kasuwarta. Wannan wata manufa ce ta Sin ta nuna cewa, ba ta neman rarar cinikayya, sai dai daidaito da adalci da cin moriyar juna, wadanda su ne muhimman abubuwan da duniya ke bukata yanzu.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Sai kuma uwa uba, soke bukatar biyan haraji da za ta fara aiwatarwa kan kasashen Afrika da ke da huldar diplomasiyya da ita. Kusan zan ce kasashen Afrika su ne kan gaba wajen cin moriyar wannan shirin na shekaru biyar-biyar domin sun samu damar shigar da karin kayayyakinsu kasuwar duniya da kara bazar kayayyakinsu zuwa sassan duniya, lamarin da zai bunkasa samar da ayyukan yi da habaka ayyukan gona da kara karfin masana’antu da kanana da matsakaitan harkokin kasuwanci da sana’o’i, lamarin da sakamakonsa zai kai ga kyautata rayuwar jama’ar nahiyar da bunkasa ci gaba.

Kamar yadda nake fada a kullum, ci gaban kasar Sin ci gaba ne ga sassan duniya ba wai barazana ba. A duk lokacin da take tsara manufofin raya kasa da inganta walwalar al’ummarta, ba ta nuna son zuciya ko neman cin nasara daga musgunawa ko matsa wa wata kasa, ta kan mayar da hankali ne wajen samar da dabaru da hanyoyin da sauran kasashe za su ci gajiya domin a gudu tare a tsira tare. Wannan ita ce ma’anar babbar kasa mai sanin ya kamata. (Fa’iza Mustapha)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Xi Ya Yi Rangadi A Sabon Yankin Xiong’an Na Lardin Hebei Dake Arewacin Kasar Sin

Xi Ya Yi Rangadi A Sabon Yankin Xiong'an Na Lardin Hebei Dake Arewacin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.