ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Twitter Space Na LEADERSHIP Hausa: Yadda ‘Yan Nijeriya Za Su Kauce Wa Komawa ‘Yar Gidan Jiya A Zaben 2023

by Sadiq
4 years ago
Yakin Neman Zabe

A hukumance a ranar Laraba aka fara yakin neman zaben jam’iyyu a Nijeriya, wanda hakan zai bai wa jam’iyyu siyasa damar tallata ‘yan takarkarunsu.

Sai dai duba da yanayi da halin da kasar nan ke ciki, ya sanya jaridar LEADERSHIP Hausa, ta shirya shiri na musamman a ‘Twitter Space’ don tattauna yadda za a magance komawa gidan jiya.

  • Gwamna Bello Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Sarkin Lokoja
  • Bazan Daukaka Kara Ba, Na Amince Da Hukuncin Kotu Akan Mazabar Yobe Ta Arewa —Lawan

Akwai matsaloli masu tarin yawa da suka shafi Nijeriya wanda suka hadar da matsalar tsaro, hauhawar farashin kayayyakin masarufi, tabarbarewar ilimi da sauran tarin matsololi.

ADVERTISEMENT

Wadannan matsaloli na daga cikin abubuwan da ‘yan siyasa za su yi amfani da su wajen yi wa ‘yan Nijeriya alkawura, wanda irin wannan wasu ‘yan siyasar suka yi a baya sannan suka kasa cika alkawuran da suka dauka.

Don guje wa fada wa irin wannan tarko, Dakta Yahuza Getso, wanda malami ne a Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya kuma masani ne kan al’amuran yau da kullum, ya samu damar shiga shirin kai tsaye, sannan ya yi fashin baki kan abubuwan da masu kada kuri’a ya kamata su yi.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Matasa Su Yi Taka-Tsantsan Da ‘Yan Siyasa

Malamin ya yi bayanin kan yadda ya kamata mutane musamman, matasa su yi taka-tsantsan da gujewa shiga sabgar da ‘yan siyasar da za su amfani da wasu wajen aikata miyagun laifuka musamman a lokutan yakin neman zabe da ma lokacin zaben.

“Matasa su ne kashin bayan al’umma yana da kyau su gujewa bin ‘yan siyasa saboda kar a yi amfani da su wajen yin barandar siyasa.”

Shi ma daga na shi bangaren shugaban dalibai Nijeriya, Usman Umar Barambu, ya nuna bacin ransa kan yadda ‘yan siyasa suka yi kunnen uwar-shegu game da yajin aikin da ASUU ke yi. Ya ce suna da kwararran matakin da za su dauka a lokacin babban zaben 2023.

Kowa da Ranarsa, Za A Zo Ranarmu

A matsayina na shugaban daliban Nijeriya, ina baka tabbacin cewar bana za ta zama daban da kowace.

Dole ne zamu zauna da kowanne dan siyasa don jin ta bakinsa kan irin abubuwan da ya tanadar mana; musamman abin da ya shafi noma, ilimi, tsaro, ayyukan yi ga matasa da sauransu.

Idan aka duba ‘yan siyasar nan musamman ‘yan takarar shugaban kasa ba wanda bai rike wani mukami a baya ba don haka, za mu yi waiwaye don ganin irin abin da ya yi sannan mu yi tunanin zabar wanda ya fi kowannensu cancanta.

Mu Ne Za Mu Gyara Kasar Nan

Mu ne muka fi kowa yawa a kasar nan, saboda muna da adadin dalibai wadanda suke Nijeriya da wadanda suke waje, muna da dalibai mutum miliyan 41. Mu ne zamu gyara Nijeriya kuma zamu bada mamaki domin za a fafata da mu.

Gwamnatin Buhari Ta Gaza Shawo Kan Matsalar Tsaro

Dakta Getso, ya kara da cewa “‘Yan takarkaru da suma fito ya kamata su fito su yi rantsuwa, cewar abin da suka yi alkawari za su cika.

Gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari ta gaza shawo kan matsalar tsaro duk da cewar kowa ya san inda wadannan masu aikata laifukan suke, dole ne a kawo karshensu, wanda ni na san inda suke kuma gwamnati ta san na san inda suke.

‘Yaki da cin hanci da rashawa, ya kamata a yi amfani da wuka daidai inda ya dace a yanka, don zartar da hukuncin da ya dace.

Daukar hukunci a kan duk wanda aka samu ya aikata daya daga cikin abubuwan dana lissafa, wanda in dai ba a yi haka ba zai yi wahala ba a sake komawa gidan jiya ba.

Shi ma wani da ya halarci shirin, ya ce abu ne mai kyau a ce mutane sun sa hankali kan kowace matsala da ta addabi kasar nan, don tantance dan takarar da ya dace su zaba.

Matara Global Ventures, tsokaci ya yi kan yadda ‘yan Nijeriya ya kamata su fahimci zamantakewa mai kyau da zaman lafiya.

Ya Kamata A Hana ‘Yan Siyasa Amfani Da Matsalar Rashin Tsaro A wajen Yakin Neman Zabe

Nahar Ishaq, cewa ya yi bai kamata ‘yan siyasa su yi amfani da matsalar rashin tsaro a wajen yakin neman zabe ba, inda ya bukaci a yi doka a hana ‘yan siyasa amfani da yanayin matsalar ta rashin tsaro. Ya ce a baya an yi irin hakan kuma babu wani sauyi da aka samu.

Dakta Getso, ya kara yin karin haske kan matsalar rashin tsaro bayan da aka masa tambaya game da gwamnatin shugaba Buhari, inda ya ce gwamnatin Buhari za ta iya magance kashi 60 zuwa 70 na matsalar tsaro.

“Ya kamata a yi doka musamman akan abin da shafi masu damara da suke aikata laifuka, wanda ba a wuce kwana 40 sai an samu wani jami’an tsaro da ya aikata laifi, gwamnati ba ta iya karya su ba. Duk inda masu laifi suke gwamnati ta san shi kuma ta san na san shi amma ta kasa tauna tsakuwa don aya ta ji tsoro.”

PDP, APC Da Sauran Jam’iyyu Duk Abu Daya Ne

Shi ma wani daga cikin wanda suka halarci shirin, ya ce yana da kyau matasa su kiyaye su san wanda za su zaba don jagoranta al’amuran matasa.

Dole Ne A Yi Yakin Neman Zabe Da Tsaro

Abdul kuwa a nasa jawabin, cewa ya yi dole ne sai an yi yakin neman zabe da matsalar rashin tsaro, saboda duba da abubuwan da suka faru sannan ga yanayin da wasu yankuna na kasar ke ciki, dole ne a bai wa dan siyasar da zai iya kawo mafita game da matsalar tsaro dama don dawowa kan turba da gujewa komawa gidan jiya.

Da yake yin dauraya game da shirin, Dakta Getso, ya bayyana cewar akwai bukatar a yi duba na tsanaki wajen zaben dan takara don gujewa cizon yatsa.

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
NECO Ta Saki Sakamakon Jarabawar 2022

NECO Ta Saki Sakamakon Jarabawar 2022

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.