Shugaban Hukumar Ƙidayar Al’umma ta Ƙasa (NPC), Dokta Aminu Yusuf Wushishi, ya rasu bayan gajeriyar rashin lafiya.
Rahotanni sun ce Wushishi ya rasu ne ranar Juma’a, 28 ga watan Agusta, 2026.
Labarin rasuwar tasa ya isa Minna, babban birnin Jihar Neja, a daidai lokacin sallar Juma’a.
Rasuwarsa ta jefa iyalansa, abokansa, abokan aikinsa da ’yan siyasa cikin jimami.
Mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Stanley Nwosu, ya tabbatar da rasuwar.
“Eh, gaskiya ne. Shugaban NPC ya rasu ne bayan gajeriyar rashin lafiya,” in ji Nwosu.
Shi ma Shugaban Sashen Kimiyya na Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Neja da ke Zungeru, Ambasada Ibrahim Umar Kontagora, ya bayyana alhininsa kan rasuwar Wushishi.
Ya bayyana marigayin a matsayin mutum mai daraja wanda gudummawar da ya bayar wajen hidimar jama’a za ta kasance cikin abubuwan da za a riƙa tunawa da shi.
“Rasuwarsa babban rashi ne ba ga iyalansa da masoyansa kaɗai ba, har ma ga al’ummar Masarautar Kontagora, Jihar Neja da Nijeriya baki ɗaya,” in ji Kontagora.
Wushishi ya fara aiki a matsayin shugaban NPC a ranar 2 ga watan Disamba, 2025, inda ya yi kusan watanni takwas riƙe da muƙamin.
Kafin naɗa shi, ya riƙe wasu muƙaman gwamnati daban-daban, sannan ya taɓa zama Sakataren Jam’iyyar PDP na Jihar Neja.
Ya maye gurbin Nasir Kwarra a matsayin shugaban hukumar.














