ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban NIS Isah Jere Ya Lashi Takobin Hukunta Jami’ai Masu Cuwa-cuwa A Hukumar

Yayin Da NIS Ta Rantsar Da Jami'anta Na Yaƙi Da Rashawa

by yahuzajere
4 years ago
NIS

Shugaban Hukumar Kula Da Shige Da Fice ta ƙasa (NIS), Isah Jere Idris ya bayyana cewa hukumar za ta ci gaba da duk wani ƙoƙari da ya wajaba wajen ganin ta magance cuwa-cuwa a ɗaukacin manya da ƙananan ofisoshinta.

  • NIS Ta Ƙaddamar Da Hukumar Gudanarwar Asusun Kula Da Baƙin Haure

Ya bayyana haka ne a yayin ƙaddamar da sabbin jami’an da aka naɗa a ɓangaren yaƙi da cin hanci da rashawa na hukumar ta NIS da ake wa laƙabi da (ACTU) a Abuja .

NIS
Jami’an Sashen Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (ACTU) yayin da ake rantsar da su.

Ya ƙara da cewa, “Ba ni da buƙatar nanata batun yadda cin hanci ke ci gaba da zama ɗaya daga cikin annobar da ke kawo cikas ga bunƙasa da ɗorewar ƙasarmu. Abin ya zama ruwan dare a kusan dukkan sassan ƙasar. A wasu lokutan ma, abubuwa na cin hanci da rashawa sun zama tamkar wata yardajjiyar ɗabi’a a cikin al’umma.

ADVERTISEMENT

“Wannan ba ƙaramin haɗari ne ba kuma ya kamata kowane mutum nagari ya yaƙi abin . Wajibi ne na faɗa muku cewa a matsayinku na ma’aikatan Sashen Yaƙi Da Cin Hanci na ACTU, kuna da jan aiki a gabanku saboda masu cin hanci za su riƙa ramuwar gayya a koyaushe amma kuma ina tabbatar muku da samun goyon bayan mahukunta domin ku samu sukunin gudanar da ayyukanku cikin nasara,” ya bayyana.

Sanarwar da ta fito daga Jami’in hulɗa da jama’a na NIS, ACI Amos Okpu ta ƙara da cewa CGI Isah Jere ya kuma yaba wa ƙoƙarin shugabannin Hukumar Yaƙi Da Rashawa ta ICPC bisa kyakkyawar alaƙar da ke tsakanin hukumomin biyu tare da yin kiran ɗorewar lamarin. Musamman ya jinjina wa yadda hukumomin suke haɗin gwiwa wajen inganta ƙwazon ma’aikata, kana ya bayyana cewa horas da ma’aikata da sake horas da su na da matuƙar muhimmanci wajen kawo ci gaban ma’aikata.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

NIS
CGI Isah Jere Idris tare da wakilin Shugaban ICPC Mista Abbia

Tun da farko, Shugaban ICPC Farfesa Bolaji Owasoneye wanda Mista Abbia Udofia ya wakilta, ya yaba wa NIS bisa namijin ƙoƙarinta wurin kafa sashen yaƙi da cin hanci da daƙile gudanar da ayyuka marasa inganci. Ya yi kira ga waɗanda aka naɗa a sashen su fahimci aikin da aka ɗora musu alhakin gudanarwa inda ya nemi su zama ababen koyi da mayar da hankali kacokan a kan ayyukansu .
Daga cikin muhimman abubuwan da aka aiwatar a wurin har da rantsuwar kama aiki wanda Barista Abodurin Adebimpe, mataimakin Babban Sufiritanda na ICPC ya karanta musu suka amsa.

NIS
Wani sashe na mahalarta taron

Bisa ƙaddamar da jami’an sashen na ACTU dai, doka ta ba su dama su sanya ido, da bincike tare da ba da rahoton duk wani abu na cin hanci a sassan hukumar ta NIS domin ɗaukar mataki.

  • https://leadership.ng/nis-issues-5683-passports-strengthens-border-security-in-niger/

Taron ƙaddamarwar ya samu halartar manyan mahukuntan NIS da manyan jami’an ICPC da suka haɗa da Mrs. Edu Davis, Babbar Jami’a a hukumar, da Larry Abwo da kuma Prisca Okwaraebo waɗanda dukkansu masu muƙamin Manyan Sufiritanda ne a ICPC da sauransu.

Ita dai Hukumar Kula Da Shige Da Fice ta Qasa (NIS) ta kasance a kan gaba wajen yaƙi da cin hanci da rashawa a tsakanin rundunonin Nijeriya masu sa kayan sarki bisa wasu muhimman abubuwa na yaki da rashawa da ta aiwatar kamar mayar da tsarin biyan kuɗin fasfo ta intanet, da cike takardun fom na neman fasfon da rajistar baƙin da ke shigowa cikin ƙasa da sauran takardu da hukumar ke bayarwa.

NIS
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Sauyin Sararin Samaniya:   Wasu ‘Yan Austireliya Sun Zaci Tashin Duniya Ya Zo

Sauyin Sararin Samaniya: Wasu ‘Yan Austireliya Sun Zaci Tashin Duniya Ya Zo

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.