• English
  • Business News
Thursday, July 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban NIS Isah Jere Ya Lashi Takobin Hukunta Jami’ai Masu Cuwa-cuwa A Hukumar

Yayin Da NIS Ta Rantsar Da Jami'anta Na Yaƙi Da Rashawa

by yahuzajere
3 years ago
in Labarai
0
Shugaban NIS Isah Jere Ya Lashi Takobin Hukunta Jami’ai Masu Cuwa-cuwa A Hukumar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Kula Da Shige Da Fice ta ƙasa (NIS), Isah Jere Idris ya bayyana cewa hukumar za ta ci gaba da duk wani ƙoƙari da ya wajaba wajen ganin ta magance cuwa-cuwa a ɗaukacin manya da ƙananan ofisoshinta.

  • NIS Ta Ƙaddamar Da Hukumar Gudanarwar Asusun Kula Da Baƙin Haure

Ya bayyana haka ne a yayin ƙaddamar da sabbin jami’an da aka naɗa a ɓangaren yaƙi da cin hanci da rashawa na hukumar ta NIS da ake wa laƙabi da (ACTU) a Abuja .

NIS
Jami’an Sashen Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (ACTU) yayin da ake rantsar da su.

Ya ƙara da cewa, “Ba ni da buƙatar nanata batun yadda cin hanci ke ci gaba da zama ɗaya daga cikin annobar da ke kawo cikas ga bunƙasa da ɗorewar ƙasarmu. Abin ya zama ruwan dare a kusan dukkan sassan ƙasar. A wasu lokutan ma, abubuwa na cin hanci da rashawa sun zama tamkar wata yardajjiyar ɗabi’a a cikin al’umma.

“Wannan ba ƙaramin haɗari ne ba kuma ya kamata kowane mutum nagari ya yaƙi abin . Wajibi ne na faɗa muku cewa a matsayinku na ma’aikatan Sashen Yaƙi Da Cin Hanci na ACTU, kuna da jan aiki a gabanku saboda masu cin hanci za su riƙa ramuwar gayya a koyaushe amma kuma ina tabbatar muku da samun goyon bayan mahukunta domin ku samu sukunin gudanar da ayyukanku cikin nasara,” ya bayyana.

Sanarwar da ta fito daga Jami’in hulɗa da jama’a na NIS, ACI Amos Okpu ta ƙara da cewa CGI Isah Jere ya kuma yaba wa ƙoƙarin shugabannin Hukumar Yaƙi Da Rashawa ta ICPC bisa kyakkyawar alaƙar da ke tsakanin hukumomin biyu tare da yin kiran ɗorewar lamarin. Musamman ya jinjina wa yadda hukumomin suke haɗin gwiwa wajen inganta ƙwazon ma’aikata, kana ya bayyana cewa horas da ma’aikata da sake horas da su na da matuƙar muhimmanci wajen kawo ci gaban ma’aikata.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

NIS
CGI Isah Jere Idris tare da wakilin Shugaban ICPC Mista Abbia

Tun da farko, Shugaban ICPC Farfesa Bolaji Owasoneye wanda Mista Abbia Udofia ya wakilta, ya yaba wa NIS bisa namijin ƙoƙarinta wurin kafa sashen yaƙi da cin hanci da daƙile gudanar da ayyuka marasa inganci. Ya yi kira ga waɗanda aka naɗa a sashen su fahimci aikin da aka ɗora musu alhakin gudanarwa inda ya nemi su zama ababen koyi da mayar da hankali kacokan a kan ayyukansu .
Daga cikin muhimman abubuwan da aka aiwatar a wurin har da rantsuwar kama aiki wanda Barista Abodurin Adebimpe, mataimakin Babban Sufiritanda na ICPC ya karanta musu suka amsa.

NIS
Wani sashe na mahalarta taron

Bisa ƙaddamar da jami’an sashen na ACTU dai, doka ta ba su dama su sanya ido, da bincike tare da ba da rahoton duk wani abu na cin hanci a sassan hukumar ta NIS domin ɗaukar mataki.

  • https://leadership.ng/nis-issues-5683-passports-strengthens-border-security-in-niger/

Taron ƙaddamarwar ya samu halartar manyan mahukuntan NIS da manyan jami’an ICPC da suka haɗa da Mrs. Edu Davis, Babbar Jami’a a hukumar, da Larry Abwo da kuma Prisca Okwaraebo waɗanda dukkansu masu muƙamin Manyan Sufiritanda ne a ICPC da sauransu.

Ita dai Hukumar Kula Da Shige Da Fice ta Qasa (NIS) ta kasance a kan gaba wajen yaƙi da cin hanci da rashawa a tsakanin rundunonin Nijeriya masu sa kayan sarki bisa wasu muhimman abubuwa na yaki da rashawa da ta aiwatar kamar mayar da tsarin biyan kuɗin fasfo ta intanet, da cike takardun fom na neman fasfon da rajistar baƙin da ke shigowa cikin ƙasa da sauran takardu da hukumar ke bayarwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Barka Da Sabuwar Shekarar Hijira: Adamu Ya Nemi ‘Yan Nijeriya Su Mallaki Katin Zaɓe

Next Post

Sauyin Sararin Samaniya: Wasu ‘Yan Austireliya Sun Zaci Tashin Duniya Ya Zo

Related

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

6 hours ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

8 hours ago
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC
Labarai

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

9 hours ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

11 hours ago
Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka
Manyan Labarai

Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka

12 hours ago
Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

14 hours ago
Next Post
Sauyin Sararin Samaniya:   Wasu ‘Yan Austireliya Sun Zaci Tashin Duniya Ya Zo

Sauyin Sararin Samaniya: Wasu ‘Yan Austireliya Sun Zaci Tashin Duniya Ya Zo

LABARAI MASU NASABA

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

July 2, 2025
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

July 2, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

July 2, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

July 2, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

July 2, 2025
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

July 2, 2025
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

July 2, 2025
Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

July 2, 2025
Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

July 2, 2025
Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

July 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.