ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban NIS Isah Jere Ya Lashi Takobin Hukunta Jami’ai Masu Cuwa-cuwa A Hukumar

Yayin Da NIS Ta Rantsar Da Jami'anta Na Yaƙi Da Rashawa

by yahuzajere
4 years ago
NIS

Shugaban Hukumar Kula Da Shige Da Fice ta ƙasa (NIS), Isah Jere Idris ya bayyana cewa hukumar za ta ci gaba da duk wani ƙoƙari da ya wajaba wajen ganin ta magance cuwa-cuwa a ɗaukacin manya da ƙananan ofisoshinta.

  • NIS Ta Ƙaddamar Da Hukumar Gudanarwar Asusun Kula Da Baƙin Haure

Ya bayyana haka ne a yayin ƙaddamar da sabbin jami’an da aka naɗa a ɓangaren yaƙi da cin hanci da rashawa na hukumar ta NIS da ake wa laƙabi da (ACTU) a Abuja .

NIS
Jami’an Sashen Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (ACTU) yayin da ake rantsar da su.

Ya ƙara da cewa, “Ba ni da buƙatar nanata batun yadda cin hanci ke ci gaba da zama ɗaya daga cikin annobar da ke kawo cikas ga bunƙasa da ɗorewar ƙasarmu. Abin ya zama ruwan dare a kusan dukkan sassan ƙasar. A wasu lokutan ma, abubuwa na cin hanci da rashawa sun zama tamkar wata yardajjiyar ɗabi’a a cikin al’umma.

ADVERTISEMENT

“Wannan ba ƙaramin haɗari ne ba kuma ya kamata kowane mutum nagari ya yaƙi abin . Wajibi ne na faɗa muku cewa a matsayinku na ma’aikatan Sashen Yaƙi Da Cin Hanci na ACTU, kuna da jan aiki a gabanku saboda masu cin hanci za su riƙa ramuwar gayya a koyaushe amma kuma ina tabbatar muku da samun goyon bayan mahukunta domin ku samu sukunin gudanar da ayyukanku cikin nasara,” ya bayyana.

Sanarwar da ta fito daga Jami’in hulɗa da jama’a na NIS, ACI Amos Okpu ta ƙara da cewa CGI Isah Jere ya kuma yaba wa ƙoƙarin shugabannin Hukumar Yaƙi Da Rashawa ta ICPC bisa kyakkyawar alaƙar da ke tsakanin hukumomin biyu tare da yin kiran ɗorewar lamarin. Musamman ya jinjina wa yadda hukumomin suke haɗin gwiwa wajen inganta ƙwazon ma’aikata, kana ya bayyana cewa horas da ma’aikata da sake horas da su na da matuƙar muhimmanci wajen kawo ci gaban ma’aikata.

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

NIS
CGI Isah Jere Idris tare da wakilin Shugaban ICPC Mista Abbia

Tun da farko, Shugaban ICPC Farfesa Bolaji Owasoneye wanda Mista Abbia Udofia ya wakilta, ya yaba wa NIS bisa namijin ƙoƙarinta wurin kafa sashen yaƙi da cin hanci da daƙile gudanar da ayyuka marasa inganci. Ya yi kira ga waɗanda aka naɗa a sashen su fahimci aikin da aka ɗora musu alhakin gudanarwa inda ya nemi su zama ababen koyi da mayar da hankali kacokan a kan ayyukansu .
Daga cikin muhimman abubuwan da aka aiwatar a wurin har da rantsuwar kama aiki wanda Barista Abodurin Adebimpe, mataimakin Babban Sufiritanda na ICPC ya karanta musu suka amsa.

NIS
Wani sashe na mahalarta taron

Bisa ƙaddamar da jami’an sashen na ACTU dai, doka ta ba su dama su sanya ido, da bincike tare da ba da rahoton duk wani abu na cin hanci a sassan hukumar ta NIS domin ɗaukar mataki.

  • https://leadership.ng/nis-issues-5683-passports-strengthens-border-security-in-niger/

Taron ƙaddamarwar ya samu halartar manyan mahukuntan NIS da manyan jami’an ICPC da suka haɗa da Mrs. Edu Davis, Babbar Jami’a a hukumar, da Larry Abwo da kuma Prisca Okwaraebo waɗanda dukkansu masu muƙamin Manyan Sufiritanda ne a ICPC da sauransu.

Ita dai Hukumar Kula Da Shige Da Fice ta Qasa (NIS) ta kasance a kan gaba wajen yaƙi da cin hanci da rashawa a tsakanin rundunonin Nijeriya masu sa kayan sarki bisa wasu muhimman abubuwa na yaki da rashawa da ta aiwatar kamar mayar da tsarin biyan kuɗin fasfo ta intanet, da cike takardun fom na neman fasfon da rajistar baƙin da ke shigowa cikin ƙasa da sauran takardu da hukumar ke bayarwa.

NIS
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Labarai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
'yansanda
Labarai

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Next Post
Sauyin Sararin Samaniya:   Wasu ‘Yan Austireliya Sun Zaci Tashin Duniya Ya Zo

Sauyin Sararin Samaniya: Wasu ‘Yan Austireliya Sun Zaci Tashin Duniya Ya Zo

LABARAI MASU NASABA

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.