ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin Sin Da Koriya Ta Arewa Sun Sha Alwashin Wanzar Da Gagarumin Kawancen Gargajiya Tsakanin Kasashen Biyu

by Sulaiman and CGTN Hausa
59 minutes ago
Sin

Babban sakataren kwamitin kolin Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kuma shugaban kasar Xi Jinping, da babban sakataren jam’iyyar ‘yan kwadago ta Koriya ta Arewa, kuma shugaban kasar Kim Jong-un, sun amince da kudurin wanzar da gagarumin kawancen gargajiya daga zuri’a zuwa zuri’a tsakanin kasashen biyu.

Shugabannin biyu su amince da wannan matsaya ne a yau Talata, yayin da shugaba Xi ke ci gaba da ziyara a Koriya ta Arewa. A kuma yau din, shugaba Xi da mai dakinsa Peng Liyuan, sun kaiwa hasumiyar kawancen Sin da Koriya ta Arewa ziyarar girmamawa, bisa rakiyar shugaba Kim da uwargidansa Ri Sol Ju.Xi da Kim, sun kuma amince cewa shekarun 1950, lokacin da Sin da Koriya ta Arewa suka yi yaki kafada da kafada, muhimman shekaru ne dake da tasiri a tarihin su. Kuma a wannan rana da safe, Xi Jinping, basa rakiyar Kim Jong-un, ya ziyarci makarantar horar da shugabannin kwamitin tsakiyar jam’iyyar KWP dake birnin Pyongyang.

Xi Jinping da Kim Jong-un sun dasa wata bishiyar fir tare. Bishiyar fir tana kasancewa koriya a duk tsawon shekara, wanda hakan ke alamta dorewar abotar Sin da Koriya ta Arewa. Bayan haka, a gaban manyan shugabannin jam’iyyu da kasashen biyu, Cai Qi da memban dindindin na ofishin siyasa na kwamitin tsakiyar KWP, kuma sakataren tsakiyar jam’iyyar Kim Jae Ryong, sun gabatar da dutsen tunawa da dasa bishiyar. A gaban dutsen, an sassaka manyan kalmomi da harsunan Sinanci da Koriya ta Arewa cewa, “Abota tsakanin Sin da Koriya ta Arewa za ta dauwama har abada”.

ADVERTISEMENT

Dadin dadawa, Xi tare da uwargidansa Peng Liyuan sun kalli wasan kwaikwayo na musamman a filin wasanni na Pyongyang a wadannan rana bisa rakiyar Kim Jong-un da uwargidansa Ri Sol-ju, tare da jama’ar Koriya ta Arewa. ‘Yan wasan kwaikwayon sun gabatar da wakoki, da raye-raye da sauran nau’o’in fasaha, don maraba da ziyarar da Xi ke yi a Koriya ta Arewa bayan shekaru 7, tare da bayyana begen su na karfafawa, da kuma bunkasa abota da hadin gwiwar gargajiya tsakanin Sin da Koriya ta Arewa.

An kammala wasan kwaikwayon da waka mai jigon “Abota tsakanin Sin da Koriya ta Arewa tana dawwama har abada.” Wakilan bangarorin Sin da Koriya ta Arewa, sun gabatar da furanni da aka aika da sunan manyan shugabannin jam’iyyun kasashen biyu, da kuma masu dakinsu ga ‘yan wasan kwaikwayon, don taya su murnar nasarar gabatar da wasan. (Saminu Alhassan、Amina Xu)

LABARAI MASU NASABA

Xi: An Cimma Matsayar Raya Dangantakar Sin Da Koriya ta Arewa A Sabon Zamani

Sin Ba Za Ta Kyale Japan Da Philippines Su Take Hakkokinta Na Ruwa Ba

Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’in Tsaro, Sun Yi Garkuwa Da Mutane Da Dama A Sokoto
  • Sulaiman
    Majalisa Ta Nemi A Haramta Shigo Da Yadiddika Domin Farfaɗo da Masaƙun Cikin Gida
  • Sulaiman
    Xi: An Cimma Matsayar Raya Dangantakar Sin Da Koriya ta Arewa A Sabon Zamani
  • Sulaiman
    A Shirye Nake In Sasanta Da Gwamnan Kano – Kwankwaso
Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi: An Cimma Matsayar Raya Dangantakar Sin Da Koriya ta Arewa A Sabon Zamani
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ba Za Ta Kyale Japan Da Philippines Su Take Hakkokinta Na Ruwa Ba
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Afrika Ta Kudu Na Ci Gaba Da Zurfafa Hadin Gwiwa A Bangaren Soji
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

MASU ALAKA

Xi: An Cimma Matsayar Raya Dangantakar Sin Da Koriya ta Arewa A Sabon Zamani
Daga Birnin Sin

Xi: An Cimma Matsayar Raya Dangantakar Sin Da Koriya ta Arewa A Sabon Zamani

June 9, 2026
Sin Ba Za Ta Kyale Japan Da Philippines Su Take Hakkokinta Na Ruwa Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ba Za Ta Kyale Japan Da Philippines Su Take Hakkokinta Na Ruwa Ba

June 9, 2026
Sin Da Afrika Ta Kudu Na Ci Gaba Da Zurfafa Hadin Gwiwa A Bangaren Soji
Daga Birnin Sin

Sin Da Afrika Ta Kudu Na Ci Gaba Da Zurfafa Hadin Gwiwa A Bangaren Soji

June 9, 2026
Next Post
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

'Yan Bindiga Sun Kashe Jami’in Tsaro, Sun Yi Garkuwa Da Mutane Da Dama A Sokoto

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’in Tsaro, Sun Yi Garkuwa Da Mutane Da Dama A Sokoto

June 9, 2026
Shugabannin Sin Da Koriya Ta Arewa Sun Sha Alwashin Wanzar Da Gagarumin Kawancen Gargajiya Tsakanin Kasashen Biyu

Shugabannin Sin Da Koriya Ta Arewa Sun Sha Alwashin Wanzar Da Gagarumin Kawancen Gargajiya Tsakanin Kasashen Biyu

June 9, 2026
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nemi A Haramta Shigo Da Yadiddika Domin Farfaɗo da Masaƙun Cikin Gida

June 9, 2026
Xi: An Cimma Matsayar Raya Dangantakar Sin Da Koriya ta Arewa A Sabon Zamani

Xi: An Cimma Matsayar Raya Dangantakar Sin Da Koriya ta Arewa A Sabon Zamani

June 9, 2026
Kwankwaso

A Shirye Nake In Sasanta Da Gwamnan Kano – Kwankwaso

June 9, 2026
Sin Ba Za Ta Kyale Japan Da Philippines Su Take Hakkokinta Na Ruwa Ba

Sin Ba Za Ta Kyale Japan Da Philippines Su Take Hakkokinta Na Ruwa Ba

June 9, 2026
Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane

Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane

June 9, 2026
Sin Da Afrika Ta Kudu Na Ci Gaba Da Zurfafa Hadin Gwiwa A Bangaren Soji

Sin Da Afrika Ta Kudu Na Ci Gaba Da Zurfafa Hadin Gwiwa A Bangaren Soji

June 9, 2026
Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin

Kwankwaso Ba Shi Da Niyyar Ficewa Daga NDC – Kwankwasiyya

June 9, 2026
Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

June 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.